ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba A Taba Zabe A Nijeriya Mai Karancin Tashe-tashen Hankula Kamar Na 2023 Ba – Gwamnatin Tarayya

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Gwamnatin Tarayya

Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa a tarihin Nijeriya ba a taba zabe mai karancin tashe-tashen hankula kamar na 2023 ba.

Ministan yada labarai da al’adu, Alhaji Lai Mohammed shi ya bayyana hakan a Birnin Washington a yayin ganawarsa da wasu cibiyoyin siyasa a babban birnin kasar Amurka.

  • Ohanaeze Ta Bukaci Tinubu Ya Saki Nnamdi Kanu Idan Aka Rantsar Da Shi

Ministan ya je Washington ne don yin tattaunawa da kafofin watsa labarai na kasa da kasa da cibiyoyin siyasa da sauransu, don samar da mafita ga kalubalen duniya.

ADVERTISEMENT

Daga cikin wadanda ministan ya tattauna da su kan zaben 2023 da aka kammala sun hada da Cibiyar Hudson, Majalisar Atlantika da Cibiyar Wilson.

Dangane da bayanan da wata gamayyar kungiyoyin farar hula a Nijeriya ta fitar, Mohammed ya ce an samu rahoton mutuwar mutane tsakanin 13 zuwa 28 a zaben da aka kammala, shi ne mafi karanci tun bayan zaben 1964/65.

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Mohammed ya ce a shekarar 1964/1965, a kalla mutane 200 ne suka mutu sakamakon rikicin zabe.
Ya ce zaben 1993, ya yi sanadiyar mutuwar mutane 100, a shekarar 1999 an samu mutuwar mutane 80, zaben 2003 ya yi sanadiyar mutuwar mutane 100, sannan an yi asarar rayuka 300 a zaben 2007.

A cewar ministan, zaben na 2011 ya yi sanadiyar mutuwar mutane 800, zaben 2015 ya yi sanadiyar mutuwar mutane 100, yayin da aka samu asarar rayuka 150 a zaben 2019.

Ministan ya jaddada muhimmacin rayuwa, inda ya bayyana cewa bai kamata dan Nijeriya ya rasa rans aba a lokacin zabe.Ya ce za a iya gudanar da zabe ba tare da rasa rai ba.

Mohammed ya ba da tabbacin cewa nan ba da dadewa ba kasar za ta kai ga matakin gudanar da zabukan kasa baki daya ba tare da an samu asarar rayuka ba.

Da yake mayar da martani ga kiraye-kirayen da ‘yan adawa suka yi na a soke zaben 2023, bisa zargin tashe-tashen hankula, ministan ya ce hakan babu adalci kuma abu ne wanda bai dace ba.

Ya ce ‘yansanda sun ba da rahoton tashe-tashen hankula da aka samu a ko’ina a kasar, amma ba su kai ga soke zaben ba.

Da yake magana kan rahoton ‘yansandan, ministan ya ce akwai kararraki 489 na laifukan zabe, sannan an kama mutum 781 da za a gurfanar da su a gaban kotu.

A cikin nazarin rahoton da ministan ya yi, ya ce an samu tashin hankali ne na kashi daya tak a sama da rumfunan zabe 300, wanda a cewarsa hakan bai wadatar ba a soke zaben.

Gwamnatin Tarayya
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Next Post
Yunwa

Samar Da Matakan Kauce Wa Yunwa A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.