Jigo a jam’iyyar APC mai mulki, Farouk Adamu Aliyu, ya ce shugaba Bola Tinubu zai sake lashe zaɓe a shekarar 2027.
Yayin hira da shirin Politics Today na gidan talabijin na Channels, Aliyu ya ce jam’iyyun adawa ba su da ƙarfi, ya kuma nuna tabbacin cewa Tinubu zai dawowa kan mulki.
- Xi: Alakar Sin Da Rasha Ta Zama Misali Na Kyakkyawar Dangantakar Manyan Kasashe
- Gwamna Yusuf Zai Kaddamar Da Majalisar Shurah Ta Jihar Kano
Ya ce shugabanci yana da ƙalubale, inda ya zargi mutane da jingina duk matsalolin ƙasar kan shugaban ƙasa.
A cewarsa, wasu daga cikin sukar da aka yi wa tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan a lokacin mulkinsa ba su dace ba.
Aliyu ya jaddada cewa: “Babu abin da zai hana Shugaba Bola Tinubu ya dawo a 2027.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp