• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Gwamna Bala Ne Ya Soke Hawan Daushe Ba – Masarautar Bauchi Ta Bayyana Gaskiya

by Khalid Idris Doya
6 months ago
in Labarai
0
Ba Gwamna Bala Ne Ya Soke Hawan Daushe Ba – Masarautar Bauchi Ta Bayyana Gaskiya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masarautar Bauchi ta bayyana cewa ba Gwamna Bala Muhammad, ba ne ya dakatar da bikin hawan Daushe na bana ba, kamar yadda ake yaɗawa a kafafen sada zumunta ba. A cewar Masarautar, kwamitin hawan ne da kansa ya rubuta buƙatar a ɗage hawan, tare da neman amincewa daga gwamnatin jihar, wadda kuma ta amsa da zuciya ɗaya.

A cikin wata sanarwa da Magatakardan Masarautar, Alh. Shehu Mudi Muhammad, ya fitar a daren Juma’a, ya jaddada cewa an samu ruɗani sakamakon rahotannin da ke nuna cewa Gwamna ne ya bayar da umarnin soke hawan.

  • Hajjin Bana: Dole A Yi Wa Maniyyatan Bauchi Riga-kafin Foliyo – Hukumar Alhazai
  • Gwamnatin Bauchi Ta Ɗage Hawan Daushe Na Sallar Bana

Sanarwar ta bayyana cewa wannan batu ba gaskiya ba ne, domin ba gwamnati ce ta nemi a dakatar da hawa ba, illa kawai ta amince da shawarar da kwamitin masarautar ya gabatar.

Masarautar ta bayyana damuwa kan yadda wasu ke ƙoƙarin ɓata sunan Gwamnan a idon jama’a, tare da kira da a dakatar da yaɗa jita-jita. Ta kuma tabbatar da kyakkyawar alaƙa da fahimta da ke tsakaninta da Gwamnan da gwamnatin sa, tare da buƙatar al’umma su ci gaba da nuna haɗin kai da mutunta al’adunsu.

Hawan Daushe dai wani muhimmin biki ne da ake gudanarwa a lokacin Sallah, inda Sarakuna da masu riƙe da muƙamai ke hawan dawakai tare da baje kolin al’adun gargajiya. Wannan hawan na taka rawa wajen ciyar da al’adu gaba da kuma ƙarfafa haɗin kan jama’a a jihar Bauchi.

Labarai Masu Nasaba

Ana Ci Gaba Da Caccakar El-rufai Kan Kalamansa Game Da Tsaron Kasa

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BauchiHawan Sallah
ShareTweetSendShare
Previous Post

Fashin Baki Kan Kasafin Kudin 2025 Na Naira Tiriliyan 54.99

Next Post

Ranar Mata Ta Duniya: NPA Ta Mayar Da Hankali Wajen Kare ‘Yancin Mata –Dantsoho

Related

Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 
Labarai

Ana Ci Gaba Da Caccakar El-rufai Kan Kalamansa Game Da Tsaron Kasa

8 hours ago
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara
Labarai

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara

9 hours ago
Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu
Labarai

Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

10 hours ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

10 hours ago
Ajandar Ci Gaban Tinubu Ta Ƙunshi Ƙasa Baki Ɗaya – Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Ajandar Ci Gaban Tinubu Ta Ƙunshi Ƙasa Baki Ɗaya – Ministan Yaɗa Labarai

10 hours ago
Muddin Nahiyar Afirka Ta Farka Ba Za A Iya Raina Ta Ba
Labarai

Yara 400,000 Ne Ke Kamuwa Da Cutar Kansa Duk Shekara A Duniya

11 hours ago
Next Post
Ranar Mata Ta Duniya: NPA Ta Mayar Da Hankali Wajen Kare ‘Yancin Mata –Dantsoho

Ranar Mata Ta Duniya: NPA Ta Mayar Da Hankali Wajen Kare ‘Yancin Mata –Dantsoho

LABARAI MASU NASABA

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

September 5, 2025
Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

September 5, 2025
Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

Ana Ci Gaba Da Caccakar El-rufai Kan Kalamansa Game Da Tsaron Kasa

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

September 5, 2025
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara

September 5, 2025
Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 5, 2025
Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

September 5, 2025
Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

September 5, 2025
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

September 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.