• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Irin Wannan Amurkar Kasashen Yankin Gabas Ta Tsakiya Suke Bukata Ba

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Ba Irin Wannan Amurkar Kasashen Yankin Gabas Ta Tsakiya Suke Bukata Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

“A yankin gabas ta tsakiya, na ji kusan kowace kasa na cewa, tana bukatar Amurka, tana bukatarmu a wajen……Tana bukatar jagorancinmu.”

Sakataren harkokin wajen kasar Amurka Anthony Blinken ke nan ya fadi haka a lokacin da ya halarci taron dandalin tattalin arzikin duniya da ya gudana a kwanan nan a birnin Davos na kasar Switzerland, kalaman da suka janyo dariya daga masu bibiyar shafukan kafofin sada zumunta na kasar Amurka, inda a shafin kafar X, suka bayyana cewa, “A’a, ba su bukata” “Amurka tuni ta ci amanarta” “Babu wanda ke bukatar sojojin mamaya na Amurka da hare-harenta”……

  • Wakiliyar Musamman Ta Shugaban Kasar Sin Ta Halarci Bikin Rantsar Da Shugaban Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo
  • An Cafke Mutumin Da Ya Kitsa Labarin Sace Kansa Don Karɓar Kuɗin Fansa Wurin Ɗan’uwansa

Kwanaki sama da 100 ke nan tun bayan barkewar rikici tsakanin Palasdinu da Isra’ila a wannan karo, lamarin da ya haifar da ci gaban tabarbarewar yanayin jin kai a yankin, rikicin da har ya tsananta halin da ake ciki a Bahar Maliya. A farkon wannan wata, Mista Blinken ya ziyarci kasashen yankin gabas ta tsakiya da dama, karkashin sunan daidaita rikici tsakanin Palasdinu da Isra’ila, sai dai a yayin ziyararsa, kusan Isra’ila ba ta taba daina hare-harenta a zirin Gaza ba, bayan ziyararsa kuma, sassan yankin na gabas ta tsakiya sai kara tsumduma cikin kazamin fada suka yi.

A hakika, tun bayan barkewar rikicin, ba ma kawai Amurka ta kara tura sojojinta zuwa yankin gabas ta tsakiya ba, har ma ta kara bayar da gudummawar soja ga kasar Isra’ila. A watan Disamban bara, sau biyu gwamnatin kasar Amurka ta sayar da makamai cikin gaggawa ga Isra’ila ba tare da samun amincewar majalisar dokokin kasar ba. Ban da haka, Amurka ta sha kawo cikas ga kokarin da ake yi na kwantar da kurar rikicin, sakamakon yadda ta kada kuri’ar rashin amincewa da kudurin tsagaita bude wuta da aka gabatar a gun kwamitin sulhun MDD.
Babu wani abu da Amurka ke kawo wa kasashen gabas ta tsakiya da ma sauran sassan duniya, illa dai yake-yake da tashin hankali da ma dakushewar tattalin arziki, sakamakon yadda take da niyyar kiyaye babakeren da ta kafa a duniya da moriyar siyasa na cin mummunar riba daga cinikin makaman soja da take yi.

In mun duba tarihin kasar na sama da tsawon shekaru 240, shekaru 16 ne kawai ba ta yaki. Da Afghanistan da Iraki da Syria da Libya da Ukraine da ma Palasdinu, tashin hankalin da ke addabar kasashe da yankuna da dama sun auku ne sakamakon kasar Amurka. Ban da haka, Amurka tana kuma dukufa a kan yayata tsare-tsarenta a duniya, inda ta sa kaimin juyin juya hali a kasashe da dama, sai dai salon dimokuradiyyarta bai dace da yanayin da kasashen da ta tilasta ma ba, matakin da ya sa suke fuskantar lalacewar harkokin siyasa da tsari. Ga kuma yadda ta yi ta kara kudin ruwa na dalarta yadda ta ga dama don kwashe ribar tattalin arzikin kasa da kasa, lallai yadda take tsananin son kai ya wadatar da kanta, amma ya lalata tsarin tattalin arzikin duniya da ma tsarin dokokin hukumar cinikayyar duniya, haka kuma ya dakile farfadowar tattalin arzikin duniya.

Labarai Masu Nasaba

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

Amurka, tuni ta zama mafarin tashin hankali na duniya.

Ba irin wannan Amurkar kasashen yankin gabas ta tsakiya suke bukata ba, ballantana ma sauran kasashen duniya. (Mai Zane:Mustapha Bulama)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Klaus Schwab: Davos Yana Fatan Duniya Ta Sake Gina Aminci

Next Post

Za A Kirkiro Manhajar Bai Wa Dalibai Bashi A Nijeriya

Related

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi
Daga Birnin Sin

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

6 hours ago
Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci
Daga Birnin Sin

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

7 hours ago
Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

9 hours ago
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

11 hours ago
An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya
Daga Birnin Sin

An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

12 hours ago
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 

14 hours ago
Next Post
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Za A Kirkiro Manhajar Bai Wa Dalibai Bashi A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

May 13, 2025
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

May 13, 2025
Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

May 13, 2025
Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

May 13, 2025
Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

May 13, 2025
Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

May 13, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

May 13, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

May 13, 2025
An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

May 13, 2025
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.