ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Irin Wannan Amurkar Kasashen Yankin Gabas Ta Tsakiya Suke Bukata Ba

by CGTN Hausa
2 years ago
Amurka

“A yankin gabas ta tsakiya, na ji kusan kowace kasa na cewa, tana bukatar Amurka, tana bukatarmu a wajen……Tana bukatar jagorancinmu.”

Sakataren harkokin wajen kasar Amurka Anthony Blinken ke nan ya fadi haka a lokacin da ya halarci taron dandalin tattalin arzikin duniya da ya gudana a kwanan nan a birnin Davos na kasar Switzerland, kalaman da suka janyo dariya daga masu bibiyar shafukan kafofin sada zumunta na kasar Amurka, inda a shafin kafar X, suka bayyana cewa, “A’a, ba su bukata” “Amurka tuni ta ci amanarta” “Babu wanda ke bukatar sojojin mamaya na Amurka da hare-harenta”……

  • Wakiliyar Musamman Ta Shugaban Kasar Sin Ta Halarci Bikin Rantsar Da Shugaban Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo
  • An Cafke Mutumin Da Ya Kitsa Labarin Sace Kansa Don Karɓar Kuɗin Fansa Wurin Ɗan’uwansa

Kwanaki sama da 100 ke nan tun bayan barkewar rikici tsakanin Palasdinu da Isra’ila a wannan karo, lamarin da ya haifar da ci gaban tabarbarewar yanayin jin kai a yankin, rikicin da har ya tsananta halin da ake ciki a Bahar Maliya. A farkon wannan wata, Mista Blinken ya ziyarci kasashen yankin gabas ta tsakiya da dama, karkashin sunan daidaita rikici tsakanin Palasdinu da Isra’ila, sai dai a yayin ziyararsa, kusan Isra’ila ba ta taba daina hare-harenta a zirin Gaza ba, bayan ziyararsa kuma, sassan yankin na gabas ta tsakiya sai kara tsumduma cikin kazamin fada suka yi.

ADVERTISEMENT

A hakika, tun bayan barkewar rikicin, ba ma kawai Amurka ta kara tura sojojinta zuwa yankin gabas ta tsakiya ba, har ma ta kara bayar da gudummawar soja ga kasar Isra’ila. A watan Disamban bara, sau biyu gwamnatin kasar Amurka ta sayar da makamai cikin gaggawa ga Isra’ila ba tare da samun amincewar majalisar dokokin kasar ba. Ban da haka, Amurka ta sha kawo cikas ga kokarin da ake yi na kwantar da kurar rikicin, sakamakon yadda ta kada kuri’ar rashin amincewa da kudurin tsagaita bude wuta da aka gabatar a gun kwamitin sulhun MDD.
Babu wani abu da Amurka ke kawo wa kasashen gabas ta tsakiya da ma sauran sassan duniya, illa dai yake-yake da tashin hankali da ma dakushewar tattalin arziki, sakamakon yadda take da niyyar kiyaye babakeren da ta kafa a duniya da moriyar siyasa na cin mummunar riba daga cinikin makaman soja da take yi.

In mun duba tarihin kasar na sama da tsawon shekaru 240, shekaru 16 ne kawai ba ta yaki. Da Afghanistan da Iraki da Syria da Libya da Ukraine da ma Palasdinu, tashin hankalin da ke addabar kasashe da yankuna da dama sun auku ne sakamakon kasar Amurka. Ban da haka, Amurka tana kuma dukufa a kan yayata tsare-tsarenta a duniya, inda ta sa kaimin juyin juya hali a kasashe da dama, sai dai salon dimokuradiyyarta bai dace da yanayin da kasashen da ta tilasta ma ba, matakin da ya sa suke fuskantar lalacewar harkokin siyasa da tsari. Ga kuma yadda ta yi ta kara kudin ruwa na dalarta yadda ta ga dama don kwashe ribar tattalin arzikin kasa da kasa, lallai yadda take tsananin son kai ya wadatar da kanta, amma ya lalata tsarin tattalin arzikin duniya da ma tsarin dokokin hukumar cinikayyar duniya, haka kuma ya dakile farfadowar tattalin arzikin duniya.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

Amurka, tuni ta zama mafarin tashin hankali na duniya.

Ba irin wannan Amurkar kasashen yankin gabas ta tsakiya suke bukata ba, ballantana ma sauran kasashen duniya. (Mai Zane:Mustapha Bulama)

Amurka
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Za A Kirkiro Manhajar Bai Wa Dalibai Bashi A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.