ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, November 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Mu San Dalilin Da ‘Yan Nijeriya Ke Son Yin Zanga-zanga Ba — Gwamnonin APC

by Sadiq
1 year ago
Zanga-zanga

Kungiyar Gwamnonin Jam’iyyar APC mai mulki, ta ce ba ta san dalilin da ya sanya ‘yan Nijeriya ke son gudanar da zanga-zanga a fadin kasar nan ba.

Da yake jawabi shugaban kungiyar gwamnonin jam’iyyar, kuma gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodinma, ya bayyana hakan ga manema labarai jim kadan bayan kammala wani taro da gwamnonin suka yi a Abuja.

  • Mangal Ya Dauki Nauyin Yi Wa Masu Ciwon Mafitsara 80 Aiki A Katsina 
  • Da Mu Za A Yi Zanga-zangar Matsin Rayuwa – NLC

“Ba mu san dalilin da ya sanya aka shirya gudanar da zanga-zanga a fadin Nijeriya ba, kuma ba mu san a kan me masu shirya zanga-zangar za su gudanar ba.

ADVERTISEMENT

“Mun gayyaci masu shirya gudanar da zanga-zangar domin mun tattauna da su, mu ji dalilinsu na shirya wannan zanga-zangar, domin mu cimma matsaya.”

A cewarsa, a matsayinsu na gwamnoni sun iya bakin kokarinsu wajen ganin, komai ya tafi yadda ya kamata a kasar nan ta hanyar magance matsalolin tsaro, farfado da tattalin arziki, tare kuma da samar da ayyukan yi ga matasa.

LABARAI MASU NASABA

Za Mu Kare Sojojin Da Ke Bakin Aiki — Ministan Tsaro

Bayanan Da Muka Samu Sun Nuna An Fara Samun Tsaro A Nijeriya – Hafsan Sojin Ƙasa

Kazalika, ya kara da cewa baya ga irin wannan kokari da suke yi bai ga dalilin gudanar da wata zanga-zanga a wannan lokaci ba.

Ana sa ran fara zanga-zangar ne a ranar 1 ga watan Agusta, wadda za ta dauki tsawon kwanaki 10 ana yi.

Masu shirya zanga-zangar na son amfani da wannan damar wajen jan hankalin gwamnati kan halin matsin rayuwa da ake ciki a Nijeriya, sakamakon cire tallafin man fetur da kuma tashin dalar Amurka da wasu sauye-sauye da aka kawo.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Za Mu Kare Sojojin Da Ke Bakin Aiki — Ministan Tsaro
Manyan Labarai

Za Mu Kare Sojojin Da Ke Bakin Aiki — Ministan Tsaro

November 12, 2025
Bayanan Da Muka Samu Sun Nuna An Fara Samun Tsaro A Nijeriya – Hafsan Sojin Ƙasa
Manyan Labarai

Bayanan Da Muka Samu Sun Nuna An Fara Samun Tsaro A Nijeriya – Hafsan Sojin Ƙasa

November 12, 2025
Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna
Manyan Labarai

Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna

November 12, 2025
Next Post
Tinubu Ya Gana Da Gwamnonin APC Kan Zanga-zangar Matsin Rayuwa

Tinubu Ya Gana Da Gwamnonin APC Kan Zanga-zangar Matsin Rayuwa

LABARAI MASU NASABA

Za Mu Kare Sojojin Da Ke Bakin Aiki — Ministan Tsaro

Za Mu Kare Sojojin Da Ke Bakin Aiki — Ministan Tsaro

November 12, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3 Tare Da Sace Babur A Nasarawa

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3 Tare Da Sace Babur A Nasarawa

November 12, 2025
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi Sama Da 200 A Katsina

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi Sama Da 200 A Katsina

November 12, 2025
Injiniya Sagir Ibrahim Ƙoƙi Ya Fice Daga Jam’iyyar NNPP

Injiniya Sagir Ibrahim Ƙoƙi Ya Fice Daga Jam’iyyar NNPP

November 12, 2025
Bayanan Da Muka Samu Sun Nuna An Fara Samun Tsaro A Nijeriya – Hafsan Sojin Ƙasa

Bayanan Da Muka Samu Sun Nuna An Fara Samun Tsaro A Nijeriya – Hafsan Sojin Ƙasa

November 12, 2025
Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna

Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna

November 12, 2025
Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

November 12, 2025
Coas

Bayan Ganawa Da Tinubu, COAS Ya Tabbatar Wa ‘Yan Nijeriya Samun Ingantaccen Tsaro

November 11, 2025
Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

November 11, 2025
Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

November 11, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.