• English
  • Business News
Monday, November 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Za A Bar Kowace Kasa A Baya Ba A Kokarinsu Na Zamanintar Da Kansu

by CGTN Hausa and Sulaiman
11 months ago
Kasa

Tun daga ranar 1 ga wannan watan da muke ciki ne kasar Sin ta soke harajin kwastam a kan dukkanin kayayyakin da take shigowa daga kasashen da suka fi fama da rashin ci gaba, wadanda suka kulla huldar diplomasiyya da ita a hukumance, ciki har da wasu kasashe 33 dake nahiyar Afirka. Hakan ya sanya ta zama kasa mai tasowa ta farko a duniya da ta dauki irin wannan mataki. A game da hakan, Dennis Munene Mwaniki, darektan zartaswa na sashen kula da harkokin Sin da Afirka karkashin cibiyar nazarin manufofin Afirka da ke kasar Kenya, ya ce, matakin da kasar Sin ta dauka na soke haraji zai taimakawa kasashe masu tasowa na fadin duniya wajen saukaka fatara da kuma gaggauta zamanintar da kansu.

 

Kasancewarta kasa mai tasowa mafi girma a duniya, kasar Sin tana sane da cewa, tabbatar da ci gaba shi ne ainihin matakin da zai taimaka wajen warware dukkanin matsaloli masu nasaba da talauci. Don haka, kasar Sin na ganin cewa, dole ne a tabbatar da bunkasuwar kasashen da suka fi fama da rashin ci gaba, a maimakon samar musu da taimako kawai.

  • Kebbi Da Brazil Zasu Yi Haɗin Gwuiwa Kan Sarrafa Nama Ta Hanyar Zamani
  • Kasar Sin Na Mai Da Hankali A Kan Halin Da Ake Ciki A Syria

Lallai, matakin da kasar Sin ta dauka a wannan karo na soke harajin kwastan, ya kasance mataki na tabbatar da bunkasuwar kasashen da suka fi fama da rashin ci gaba. Sanin kowa ne kasashen ba sa rasa kayayyaki masu inganci, sai dai sun kasa samun damar shiga kasuwannin duniya, wasu kuma sabo da yawan kudin da za su biya don fitar da kayayyakinsu zuwa ketare. Ga shi yanzu, yadda kasar Sin ta soke harajin kwastan ya samar da kyawawan sharudda ga kasashen da matakin ya shafa wajen fitar da kayayyakinsu masu inganci zuwa kasar Sin, kuma hakan tabbas zai sa kaimin bunkasuwar sana’o’in kasashen, tare da sa kaimi ga samar da guraben aikin yi da saukaka fatara. Muna iya hasashen cewa, bisa ga matakin, kayayyaki masu inganci na kasashen da suka fi fama da rashin ci gaba a Afirka, ciki har da abarba na Benin da gahawa na Habasha da tattasai na Rwanda da zuma na Tanzania, sai kuma naman rago na Madagarscar, za su gaggauta shiga babbar kasuwar kasar Sin, wanda hakan zai samar musu babbar damar tabbatar da ci gabansu.

 

LABARAI MASU NASABA

A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

Zamanintar da kansu buri daya ne ga Sin da kasashen Afirka da ma sauran kasashe masu tasowa. A lokacin da take kokarin zamanintar da kanta, kasar Sin ba ta son ganin ita kadai ta cimma burinta, a maimakon haka, tana son ganin kowa burinsa ya cika. Don haka, a lokacin da take raya kanta, har kullum kasar Sin na dukufa a kan raba damammakinta ga kasashen Afirka da ma sauran kasashe masu tasowa. Hakika, ban da matakin nan na soke harajin kwastan, ta kuma samar da kafar musamman ga kayayyakin amfanin gona da kasashen Afirka ke fitarwa zuwa gare ta, tare da samar da sauki ga kamfanonin kasashen Afirka wajen halartar bukukuwan baje kolin da ta shirya, irinsu bikin baje kolin kayayyaki da suke shigowa daga ketare, baya ga haka, ta kuma samar musu taimako wajen horar da kwararru, da dai sauransu.

 

A gun taron kolin dandalin tattaunawar hadin gwiwa a tsakanin Sin da kasashen Afirka da aka gudanar a watan Satumban bana a birnin Beijing, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da jawabin cewa, ba za a bar kowace kasa a baya ba a kokarin da suke yi na zamanintar da kansu. Dukkanin kasashen Sin da Afirka da ma sauran kasashe masu tasowa, sai mu hada karfi da karfe, domin cimma wannan burinmu na bai daya. (Lubabatu)

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?
Ra'ayi Riga

A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?

November 2, 2025
Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani
Ra'ayi Riga

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

October 28, 2025
Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

October 27, 2025
Next Post
Dokar Haraji: Ƙarawa Masu Kudi Haraji Ba Talakawa Ba Shi Ya Kamata

Dokar Haraji: Ƙarawa Masu Kudi Haraji Ba Talakawa Ba Shi Ya Kamata

LABARAI MASU NASABA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa

Mayar Da Martani Kan Barazanar Amurka Ga Nijeriya: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yaba Wa Kwankwaso 

November 3, 2025
Likitoci

NARD Ta Yi Fatali Da Iƙirarin Gwamnatin Tarayya Na Ba Ta ₦43bn, Kuma Yajin Aiki Na Nan

November 3, 2025
Kano

Kano Ta Amince Da Naira Biliyan 8.2 Don Ayyukan ilimi, Samar Da Ruwa, Da Makamashi

November 3, 2025
Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

November 2, 2025
Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

November 2, 2025
Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

November 2, 2025
Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

November 2, 2025
Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

November 2, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.