ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Za A Bar Kowace Kasa A Baya Ba A Kokarinsu Na Zamanintar Da Kansu

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Kasa

Tun daga ranar 1 ga wannan watan da muke ciki ne kasar Sin ta soke harajin kwastam a kan dukkanin kayayyakin da take shigowa daga kasashen da suka fi fama da rashin ci gaba, wadanda suka kulla huldar diplomasiyya da ita a hukumance, ciki har da wasu kasashe 33 dake nahiyar Afirka. Hakan ya sanya ta zama kasa mai tasowa ta farko a duniya da ta dauki irin wannan mataki. A game da hakan, Dennis Munene Mwaniki, darektan zartaswa na sashen kula da harkokin Sin da Afirka karkashin cibiyar nazarin manufofin Afirka da ke kasar Kenya, ya ce, matakin da kasar Sin ta dauka na soke haraji zai taimakawa kasashe masu tasowa na fadin duniya wajen saukaka fatara da kuma gaggauta zamanintar da kansu.

 

Kasancewarta kasa mai tasowa mafi girma a duniya, kasar Sin tana sane da cewa, tabbatar da ci gaba shi ne ainihin matakin da zai taimaka wajen warware dukkanin matsaloli masu nasaba da talauci. Don haka, kasar Sin na ganin cewa, dole ne a tabbatar da bunkasuwar kasashen da suka fi fama da rashin ci gaba, a maimakon samar musu da taimako kawai.

ADVERTISEMENT
  • Kebbi Da Brazil Zasu Yi Haɗin Gwuiwa Kan Sarrafa Nama Ta Hanyar Zamani
  • Kasar Sin Na Mai Da Hankali A Kan Halin Da Ake Ciki A Syria

Lallai, matakin da kasar Sin ta dauka a wannan karo na soke harajin kwastan, ya kasance mataki na tabbatar da bunkasuwar kasashen da suka fi fama da rashin ci gaba. Sanin kowa ne kasashen ba sa rasa kayayyaki masu inganci, sai dai sun kasa samun damar shiga kasuwannin duniya, wasu kuma sabo da yawan kudin da za su biya don fitar da kayayyakinsu zuwa ketare. Ga shi yanzu, yadda kasar Sin ta soke harajin kwastan ya samar da kyawawan sharudda ga kasashen da matakin ya shafa wajen fitar da kayayyakinsu masu inganci zuwa kasar Sin, kuma hakan tabbas zai sa kaimin bunkasuwar sana’o’in kasashen, tare da sa kaimi ga samar da guraben aikin yi da saukaka fatara. Muna iya hasashen cewa, bisa ga matakin, kayayyaki masu inganci na kasashen da suka fi fama da rashin ci gaba a Afirka, ciki har da abarba na Benin da gahawa na Habasha da tattasai na Rwanda da zuma na Tanzania, sai kuma naman rago na Madagarscar, za su gaggauta shiga babbar kasuwar kasar Sin, wanda hakan zai samar musu babbar damar tabbatar da ci gabansu.

 

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

Zamanintar da kansu buri daya ne ga Sin da kasashen Afirka da ma sauran kasashe masu tasowa. A lokacin da take kokarin zamanintar da kanta, kasar Sin ba ta son ganin ita kadai ta cimma burinta, a maimakon haka, tana son ganin kowa burinsa ya cika. Don haka, a lokacin da take raya kanta, har kullum kasar Sin na dukufa a kan raba damammakinta ga kasashen Afirka da ma sauran kasashe masu tasowa. Hakika, ban da matakin nan na soke harajin kwastan, ta kuma samar da kafar musamman ga kayayyakin amfanin gona da kasashen Afirka ke fitarwa zuwa gare ta, tare da samar da sauki ga kamfanonin kasashen Afirka wajen halartar bukukuwan baje kolin da ta shirya, irinsu bikin baje kolin kayayyaki da suke shigowa daga ketare, baya ga haka, ta kuma samar musu taimako wajen horar da kwararru, da dai sauransu.

 

A gun taron kolin dandalin tattaunawar hadin gwiwa a tsakanin Sin da kasashen Afirka da aka gudanar a watan Satumban bana a birnin Beijing, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da jawabin cewa, ba za a bar kowace kasa a baya ba a kokarin da suke yi na zamanintar da kansu. Dukkanin kasashen Sin da Afirka da ma sauran kasashe masu tasowa, sai mu hada karfi da karfe, domin cimma wannan burinmu na bai daya. (Lubabatu)

 

Kasa
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
Kasa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Next Post
Dokar Haraji: Ƙarawa Masu Kudi Haraji Ba Talakawa Ba Shi Ya Kamata

Dokar Haraji: Ƙarawa Masu Kudi Haraji Ba Talakawa Ba Shi Ya Kamata

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.