ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Za A Bar Kowace Kasa A Baya Ba A Kokarinsu Na Zamanintar Da Kansu

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Kasa

Tun daga ranar 1 ga wannan watan da muke ciki ne kasar Sin ta soke harajin kwastam a kan dukkanin kayayyakin da take shigowa daga kasashen da suka fi fama da rashin ci gaba, wadanda suka kulla huldar diplomasiyya da ita a hukumance, ciki har da wasu kasashe 33 dake nahiyar Afirka. Hakan ya sanya ta zama kasa mai tasowa ta farko a duniya da ta dauki irin wannan mataki. A game da hakan, Dennis Munene Mwaniki, darektan zartaswa na sashen kula da harkokin Sin da Afirka karkashin cibiyar nazarin manufofin Afirka da ke kasar Kenya, ya ce, matakin da kasar Sin ta dauka na soke haraji zai taimakawa kasashe masu tasowa na fadin duniya wajen saukaka fatara da kuma gaggauta zamanintar da kansu.

 

Kasancewarta kasa mai tasowa mafi girma a duniya, kasar Sin tana sane da cewa, tabbatar da ci gaba shi ne ainihin matakin da zai taimaka wajen warware dukkanin matsaloli masu nasaba da talauci. Don haka, kasar Sin na ganin cewa, dole ne a tabbatar da bunkasuwar kasashen da suka fi fama da rashin ci gaba, a maimakon samar musu da taimako kawai.

ADVERTISEMENT
  • Kebbi Da Brazil Zasu Yi Haɗin Gwuiwa Kan Sarrafa Nama Ta Hanyar Zamani
  • Kasar Sin Na Mai Da Hankali A Kan Halin Da Ake Ciki A Syria

Lallai, matakin da kasar Sin ta dauka a wannan karo na soke harajin kwastan, ya kasance mataki na tabbatar da bunkasuwar kasashen da suka fi fama da rashin ci gaba. Sanin kowa ne kasashen ba sa rasa kayayyaki masu inganci, sai dai sun kasa samun damar shiga kasuwannin duniya, wasu kuma sabo da yawan kudin da za su biya don fitar da kayayyakinsu zuwa ketare. Ga shi yanzu, yadda kasar Sin ta soke harajin kwastan ya samar da kyawawan sharudda ga kasashen da matakin ya shafa wajen fitar da kayayyakinsu masu inganci zuwa kasar Sin, kuma hakan tabbas zai sa kaimin bunkasuwar sana’o’in kasashen, tare da sa kaimi ga samar da guraben aikin yi da saukaka fatara. Muna iya hasashen cewa, bisa ga matakin, kayayyaki masu inganci na kasashen da suka fi fama da rashin ci gaba a Afirka, ciki har da abarba na Benin da gahawa na Habasha da tattasai na Rwanda da zuma na Tanzania, sai kuma naman rago na Madagarscar, za su gaggauta shiga babbar kasuwar kasar Sin, wanda hakan zai samar musu babbar damar tabbatar da ci gabansu.

 

LABARAI MASU NASABA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

Zamanintar da kansu buri daya ne ga Sin da kasashen Afirka da ma sauran kasashe masu tasowa. A lokacin da take kokarin zamanintar da kanta, kasar Sin ba ta son ganin ita kadai ta cimma burinta, a maimakon haka, tana son ganin kowa burinsa ya cika. Don haka, a lokacin da take raya kanta, har kullum kasar Sin na dukufa a kan raba damammakinta ga kasashen Afirka da ma sauran kasashe masu tasowa. Hakika, ban da matakin nan na soke harajin kwastan, ta kuma samar da kafar musamman ga kayayyakin amfanin gona da kasashen Afirka ke fitarwa zuwa gare ta, tare da samar da sauki ga kamfanonin kasashen Afirka wajen halartar bukukuwan baje kolin da ta shirya, irinsu bikin baje kolin kayayyaki da suke shigowa daga ketare, baya ga haka, ta kuma samar musu taimako wajen horar da kwararru, da dai sauransu.

 

A gun taron kolin dandalin tattaunawar hadin gwiwa a tsakanin Sin da kasashen Afirka da aka gudanar a watan Satumban bana a birnin Beijing, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da jawabin cewa, ba za a bar kowace kasa a baya ba a kokarin da suke yi na zamanintar da kansu. Dukkanin kasashen Sin da Afirka da ma sauran kasashe masu tasowa, sai mu hada karfi da karfe, domin cimma wannan burinmu na bai daya. (Lubabatu)

 

Kasa
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya
Kasa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

MASU ALAKA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

May 29, 2026
Next Post
Dokar Haraji: Ƙarawa Masu Kudi Haraji Ba Talakawa Ba Shi Ya Kamata

Dokar Haraji: Ƙarawa Masu Kudi Haraji Ba Talakawa Ba Shi Ya Kamata

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.