• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Zamu Rufe Rijistar Zabe Ba Har Sai Abinda Hali Ya Yi – Shugaban INEC

bySulaiman
3 years ago
Inec

Shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, ya bayyana cewa ba za a rufe rajistar zaɓe ba har sai hukumar ta gamsu da cewa jama’a sun yi amfani da damar ƙarin wa’adin da za ta yi, sun yi rajista sosai.

Yakubu ya ce saboda haka mutane su kwantar da hankalin su, INEC ba za ta rufe yin rajistar zaɓe ba a ranar 30 ga Yuni, 2022.

  • 2023: INEC Ta Kara Wa’adin Yin Rajistar Katin Zabe

Shugaban ya yi wannan albishir ne yayin da ya ke wa dandazon matasa jawabi a Tsohon Dandalin Fareti a Abuja.

Inec
Shugaban hukumar INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, Kwamishinonin hukumar, Sakataren Hukumar, tare da sauran jama’a a wurin taron da ya gudana a tsohon filin fareti na kasa da ke Abuja

Matasan dai sun taru ne domin halartar gangamin wayar wa da matasa kai kan muhimmancin yin rajista.

INEC ce ta shirya gangamin tare da haɗin-gwiwar ƙungiyar bin diddigin zaɓe ta ‘Yiaga Africa’, kuma Ƙungiyar Tarayyar Turai ce ta ɗauki nauyin shirya taron.

LABARAI MASU NASABA

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

A jawabin sa da ya ke yi a ranar Asabar, Yakubu ya ce, “Ku na so ku sani ko INEC za ta rufe yin rajista nan da kwanaki biyar? To a madadin INEC ina tabbatar maku da cewa ba za a rufe rajista ba har sai mun gamsu da cewa yawan jama’ar da mu ke son ganin sun mallaki rajistar zaɓe duk sun samu dama sun yi rajista.”

Yakubu ya ce nan ba da daɗewa ba INEC za ta fitar ranar da za daina rajista.

Yayin da ya ke ƙarin haske kan cigaban da ake samu wajen aikin rajista, ya ce a cikin kwana biyar cakal da ake rajista a cikin Tsohon Filin Fareti, an yi wa mutum fiye da 14,000 rajista.

A wani labarin makamancin wannan, Farfesa Yakubu ya jaddada cewa INEC za ta ƙara yawan na’urorin rajistar zaɓe a dukkan jihohin ƙasar nan.

Ya ce INEC za ta ƙara wa’adin yin rajista domin tabbatar da cewa ta bai wa ɗimbin ‘yan Nijeriya isasshen lokacin yin rajista, ta yadda jama’a da dama za su samu jefa ƙuri’a a zaɓen 2023.

Inec

Ya ce: “Mun raba ƙarin na’urorin yin rajista zuwa jihohi a wannan makon, kuma yanzu ma za a ƙara aikawa da su a wasu wuraren tsakanin Litinin zuwa Juma’a.”

Lokacin da ya ke amsa jinjinar da dandazon matasa su ka riƙa yi, su na cewa, “Ba ma son maguɗin zaɓe”, Yakubu ya tabbatar masu da cewa, “Zaɓen gwamnan Jihar Ekiti da aka yi a makon jiya ya yi kyau. Na gwamnan Jihar Osun da za a yi nan gaba zai fi na Osun kyau. Shi kuma zaɓen 2023 zai fi kowane sahihanci.”

Inec

A jawabin sa, Jakaden Tarayyar Turai a Najeriya da ECOWAS, Samuel Isipi, ya yi kira ga ‘yan Nijeriya da kada su riƙa sayar da ƙuri’un su ga ‘yan siyasa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
PDP Ta Ja Kunnen Tsohon Shugaban Kasa, Obasanjo Kan Dan Takararta

PDP Ta Ja Kunnen Tsohon Shugaban Kasa, Obasanjo Kan Dan Takararta

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version