ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Zamu Rufe Rijistar Zabe Ba Har Sai Abinda Hali Ya Yi – Shugaban INEC

by Sulaiman
4 years ago
Inec

Shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, ya bayyana cewa ba za a rufe rajistar zaɓe ba har sai hukumar ta gamsu da cewa jama’a sun yi amfani da damar ƙarin wa’adin da za ta yi, sun yi rajista sosai.

Yakubu ya ce saboda haka mutane su kwantar da hankalin su, INEC ba za ta rufe yin rajistar zaɓe ba a ranar 30 ga Yuni, 2022.

  • 2023: INEC Ta Kara Wa’adin Yin Rajistar Katin Zabe

Shugaban ya yi wannan albishir ne yayin da ya ke wa dandazon matasa jawabi a Tsohon Dandalin Fareti a Abuja.

ADVERTISEMENT
Inec
Shugaban hukumar INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, Kwamishinonin hukumar, Sakataren Hukumar, tare da sauran jama’a a wurin taron da ya gudana a tsohon filin fareti na kasa da ke Abuja

Matasan dai sun taru ne domin halartar gangamin wayar wa da matasa kai kan muhimmancin yin rajista.

INEC ce ta shirya gangamin tare da haɗin-gwiwar ƙungiyar bin diddigin zaɓe ta ‘Yiaga Africa’, kuma Ƙungiyar Tarayyar Turai ce ta ɗauki nauyin shirya taron.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

A jawabin sa da ya ke yi a ranar Asabar, Yakubu ya ce, “Ku na so ku sani ko INEC za ta rufe yin rajista nan da kwanaki biyar? To a madadin INEC ina tabbatar maku da cewa ba za a rufe rajista ba har sai mun gamsu da cewa yawan jama’ar da mu ke son ganin sun mallaki rajistar zaɓe duk sun samu dama sun yi rajista.”

Yakubu ya ce nan ba da daɗewa ba INEC za ta fitar ranar da za daina rajista.

Yayin da ya ke ƙarin haske kan cigaban da ake samu wajen aikin rajista, ya ce a cikin kwana biyar cakal da ake rajista a cikin Tsohon Filin Fareti, an yi wa mutum fiye da 14,000 rajista.

A wani labarin makamancin wannan, Farfesa Yakubu ya jaddada cewa INEC za ta ƙara yawan na’urorin rajistar zaɓe a dukkan jihohin ƙasar nan.

Ya ce INEC za ta ƙara wa’adin yin rajista domin tabbatar da cewa ta bai wa ɗimbin ‘yan Nijeriya isasshen lokacin yin rajista, ta yadda jama’a da dama za su samu jefa ƙuri’a a zaɓen 2023.

Inec

Ya ce: “Mun raba ƙarin na’urorin yin rajista zuwa jihohi a wannan makon, kuma yanzu ma za a ƙara aikawa da su a wasu wuraren tsakanin Litinin zuwa Juma’a.”

Lokacin da ya ke amsa jinjinar da dandazon matasa su ka riƙa yi, su na cewa, “Ba ma son maguɗin zaɓe”, Yakubu ya tabbatar masu da cewa, “Zaɓen gwamnan Jihar Ekiti da aka yi a makon jiya ya yi kyau. Na gwamnan Jihar Osun da za a yi nan gaba zai fi na Osun kyau. Shi kuma zaɓen 2023 zai fi kowane sahihanci.”

Inec

A jawabin sa, Jakaden Tarayyar Turai a Najeriya da ECOWAS, Samuel Isipi, ya yi kira ga ‘yan Nijeriya da kada su riƙa sayar da ƙuri’un su ga ‘yan siyasa.

Inec
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
PDP Ta Ja Kunnen Tsohon Shugaban Kasa, Obasanjo Kan Dan Takararta

PDP Ta Ja Kunnen Tsohon Shugaban Kasa, Obasanjo Kan Dan Takararta

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.