A yau Talata, an kaddamar da taron sabbin kafofin yada labaru na kasar Sin na shekarar 2022 a birnin Changsha dake tsakiyar kasar, inda Huang Kunming, babban jami’i mai kula da harkokin yada labaru na kasar, ya halarci bikin bude taron ta kafar bidiyo, gami da gabatar da jawabi.
A cewarsa, ya kamata a kara yin nazari kan dabaru masu alaka da aikin yada labaru, da sabbin fasahohi na zamanin da muke ciki. Sa’an nan a hanzarta raya bangaren sabbin nau’ikan kafofin yada labaru, don taimakawa kokarin raya kasa. (Bello Wang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp