• English
  • Business News
Wednesday, June 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babbar Kotun Tarayyar Kaduna Ta Sa Ranar Sauraron Karar Wasu Mahajjata Kan Hajjin 2024

by Abubakar Abba
6 months ago
in Labarai
0
Babbar Kotun Tarayyar Kaduna Ta Sa Ranar Sauraron Karar Wasu Mahajjata Kan Hajjin 2024
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babbar Kotun Tarayya mai lamba daya dake da zamanta a Jihar Kaduna Daura da ND, wacce mai Shari’a R.M. Aikawa, ke alkalanci, ta fara sauraran karar da wasu mahajjatan shekara ta 2024 su 64.

Mahajjatan sun dai maka Hukumar Alhazai ta kasa (NAHCON) ne tare da Hukumar Alhazain ta Jihar Kaduna a kan wasu hakkokinsu, da ba su cika musu ba a ya yin da suke gudanar da aikin hajjin na 2024.

  • Hajji 2025: NAHCON Ta Tantance Kamfanonin Jiragen Da Za Su Yi Jigilar Alhazai Zuwa Saudiyya
  • Kotu Ta Bayar Da Belin Yahaya Bello Kan Naira Miliyan 500

A hirarsa da manema labarai jim kadan bayan tashi daga zaman kotun, Barista Bashir Musa lauyan masu kara ya ce, “ Mun zo kotu ne, sakamakon mutanen da muke tsayawa a matsayin su na mahajjata da suka biya kudaden su na zuwa aikin hajji ta karkashin Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kaduna na shekarar 2024.”

Ya ce, wadanda muka tsayawa, sun rubuta wata takarda, suna bukatar sanin yadda aka yi kudadensu aka kashe su a lokacin aikin hajjin na 2024, ga su hukumar aikin hajji ta kasa da kuma ta Jihar Kaduna, wato suna bukatar wadannan hukumomin biyu, su bayani ta yaya aka yi da kudadensu da kuma yadda aka yi da Naira biliyan 90 wanda Gwamnatin Tarayya ta bayar a matsayin kudin tallafi na aikin hajjin na 2024, sakamakon yanayin yadda aka yi musu a Saudiyya, yadda aka karbe su a Saudiyya da yadda suka gabatar da aikin na su.”

Bashir ya ci gaba da cewa,“Wadnda muke tsayawar, akwai tambayoyi da suke da su akan yadda aka yi da wannan kudin, saboda ba a ba su kulawa yadda ya kamata ba a lokacin da suka kaddamar da aikin hajjin.”

Labarai Masu Nasaba

Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida

KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

Ya kara da cewa, da suka rubuta, har zuwa yau, an bayar da kwanuka 30 ga wadannan hukumomin, amma ba su iya bayar da wadannan bayanai a rubuce ba, shi ya sa muka garzaya zuwa kotu, domin kotun ta sanya su, na farko dai, muna son mu sani daga kotun shin ma muna da ‘yanci? To kotu ta sanya su tilas hukumomin su bayar da wadannan dalilan a kan yadda aka yi da wadannan kudaden a rubuce.

Ya sanar da cewa, wadanda suka shigar karar su 64 ne, domin wadannan bukatun, inda ya ce, iya sanin mu a cikin wadannan masu karar  kowanne daya babu wanda ya biya kasa da Naira miliyan shida da dari shida da ‘yan kai na aikin hajjin na bana.

Bashir ya sanar da cewa, a zaman farko da kotun ta yi kan karar, amma Lauyan hukumar jin dadin Alhazai ta Jihar Kaduna suka aiko da takarda, suna bukatar a daga musu zuwa zaman kotun na gaba domin a yanzu suna gaban wata kotu, mu kuma ganin cewa wannan ne zama na farko sai muka ba su uzuri ba mu kalubalanci bukatar su ba, amma muna so su zo mu zauna, aji muhawarar ko wanne bangare.

A cewrsa, “ Fatanmu shi ne, su kawo dalilan da suka hana su duba wannan takarda da muka rubuta musu wanda kuma a karshe muna son kotu ta duba, idan wannan yanayin ya bukaci a sanya su su biya mu wasu kudade na wahalhalun da muka sha kotu ta sanya su su biya mu.

Kotun ta sanya ranar 21 na watan Janairu 2025 domin a dawo a saurari wannan sharia’ar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hajji
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dabaru Da Fasahohin Sin Na Taimakawa Kasashen Afirka Wajen Tinkarar Kwararar Hamada

Next Post

Xi: Mahukuntan Tsakiya Suna Ba Da Cikakken Goyon Baya Ga HK Wajen Inganta Sabon Yanayin Tattalin Arziki

Related

Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida
Labarai

Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida

35 minutes ago
KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano
Manyan Labarai

KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

3 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara

5 hours ago
Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano
Manyan Labarai

Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano

6 hours ago
Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

14 hours ago
Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato
Labarai

Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

15 hours ago
Next Post
Xi: Mahukuntan Tsakiya Suna Ba Da Cikakken Goyon Baya Ga HK Wajen Inganta Sabon Yanayin Tattalin Arziki

Xi: Mahukuntan Tsakiya Suna Ba Da Cikakken Goyon Baya Ga HK Wajen Inganta Sabon Yanayin Tattalin Arziki

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida

Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida

June 25, 2025
Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi

Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi

June 25, 2025
KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

June 25, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara

‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara

June 25, 2025
Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano

Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano

June 25, 2025
Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

June 24, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

June 24, 2025
Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

June 24, 2025
Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

June 24, 2025
Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

June 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.