• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Batun Bayyana Sakamakon Zabe Ta Na’ura A Cikin Dokar Zabe –Lawan

byYusuf Shuaibu
3 years ago
Lawan

Shugaban majalisan dattawa, Ahmad Lawan ya yi ikirarin cewa tun asali babu batun bayyana sakamakon zabe ta na’urar BVAS a cikin dokar zabe ta shekarar 2022.

Lawan ya yi wannan ikirarin ne a lokacin da yake bayar da gudunmuwarsa kan kudirin da Sanata Ibrahim Oloriegbe, mai wakiltar mazabar Kwara ta tsakiya a karkashin jam’iyyar APC ya yi kan ce-ce-ku-cen da ya biyo bayan zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya na ranar 25 ga watan Fabrairu kan kin yin amfani da bayyana sakamakon zabe ta na’urar BVAS.

  • Zaben 2023: Bazatar Da Aka Samu A Majalisar Kasa

Shugaban majalisar dattawan, ya ce abin da majalisar ta amince da shi ne na tattara sakamakon zabe da kuma mika shi ga hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC).

A cikin kudurin na Sanata Oloriegbe, ya bukaci majalisar dattijai ta bukaci dukkanin masu ruwa da tsaki na siyasa, shugabanni da kowane dan Nijeriya da su kwantar da hankalinsu, su bar batun maganar bayyana sakamakon zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisar dokokin kasar, bisa tanadin dokar zabe.

Sanata Sani Musa, daga Jihar Neja, ya ce tun da ‘yan Nijeriya ba su yi zabe ta hanyar bayyana sakamakon zabe ta na’ura ba, batun neman INEC ta aika da sakamakon ta hanyar lantarki bai zama dole ba, saboda dokar zabe ba ta umurci hukumar zabe ta yi hakan ba.

LABARAI MASU NASABA

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

Sai dai mahawarar ta haifar da ce-ce-ku-ce a tsakanin ‘yan majalisar bisa tsarin jam’iyyar, saboda sabanin ra’ayi da sanatocin PDP suka yi, inda suka bukaci a janye kudirin.

Shugaban marasa rinjaye na majalisar dattawa, Sanata Chukwuka Utazi, a lokacin da yake bayar da kudirinsa, ya bukaci hukumar zabe ta INEC da ta bi dokar zabe kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanada.

Da yake jawabi, Sanata Uche Ekwunife, jigo a jam’iyyar PDP, mai wakiltan Anambra ta tsakiya, ya dage da cewa ya kamata INEC ta bi tsarin dokar zabe.

Sanata Biodun Olujimi, wanda shi ma dan jam’iyyar adawa ta PDP ne, ya yi kira da a samar da zaman lafiya, inda ya bukaci ‘yan Nijeriya da su kwantar da hankula ta yadda za a shawo kan lamarin ba tare da jefa kasar cikin rudani ba.

Bugu da kari, Sanata Opeyemi Bamidele na jam’iyyar APC mai mulki a lokacin da yake magana kan batun, ya bukaci INEC da ta yi abin da ya dace bisa tanadin dokar zabe, inda ya yi kira ga ‘yan Nijeriya da su yi hakuri har INEC ta samu damar kammala aikin zabe gaba daya.

Ya kuma yi kira ga bangaren shari’a da su yi abin da ya dace, inda ya yi nuni da cewa matukar dai an yi abin da ya dace, za a shawo kan duk wata hargitsi wanda za ta wanzar da zaman lafiya.

Mataimakin mai tsawatarwa na majalisar dattawa, Aliyu Sabi, a nasa jawabin ya yi kira ga ‘yan Nijeriya da su bari a ci gaba da gudanar da aikin domin a karfafa dimokuradiyya.

Da yawa daga cikin ‘yan majalisar sun ba da gudunmawa, domin nuna goyon bayansu ga kudirin, wanda ya kai ga amincewa da shi, bayan da shugaban majalisar ya kada kuri’a.

A jawabinsa na rufe kudirin, Lawan ya bukaci duk wanda bai gamsu da hukuncin da INEC ta yanke ba da ya garzaya kotu, amma ka da ya kawo matsala a kasar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
Mutum 25 Ne Suka Bace Cikin Wata 6 A Jihar Abia — ‘Yan Sanda

'Yansanda Sun Tabbatar Da Mutuwar Mutum 12 Yayin Tashin Bam A Wurin Hako Danyen Mai A Ribas

LABARAI MASU NASABA

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version