ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben 2023: Bazatar Da Aka Samu A Majalisar Kasa

by Idris Aliyu Daudawa
3 years ago
majalisar kasa

Zaben ‘yan majalisun kasa da suka hada dana Dattawa da Wakilai an gabatar da shi ne tare da na Shugaban kasa wanda aka yi shi ranar Asabar ta makon daya gabata a duk fadin tarayyar Nijeriya.Ko shakka babu sakamkon zaben ya bada mamaki ga wadansu ‘yan majalisun da suka tsaya takara da maida majalisun biyu tamkar gidajensu na gado.

Hausawa dama sun ce ta faru ta kare an yi wa mai zane daya sata, wasu har ya zuwa wannan lokaci da ake ciki suna cikin yanayi na mamaki da kuma kamar dimaucewa,domin kuwa wasu daga cikinsu basu taba tsammanin irin wannan rana zata iya riskarsu ba, ba tare da sun yi shirin barin inda suke ba.

  • Gwamnatin Yobe Za Ta bai Wa Malamai Bashin N500m Don Yi Noma

Ita dama rayuwa haka take kasancewa saboda, kuwa shi mutum ya san ‘ko ba dade ko ba jima watarana ba wataran bace.Al’amarin duniya dama fararrene kuma kararrene saboda dai ko ba komai mutum ya san yadda ya tashi ya ga yadda yake a gidansu,tun yana cikin abinda aka sa aka rufe masa jiki bayan an haife shi, tun bai iya komai ba,har ga shi shine Allah ya kai shi wani wurin da bai taba ko ma mafarkin zai iya zuwa can ba.

ADVERTISEMENT

Duniyar ma da daya- daya ne aka zota hakanan kuma za’ a barta kowa ya komawa wanda ya halicce shi, saboda ai ya san ba shine ya halicci kan shi ba Allah Subhanu Wata’ala ne ya amince har ma ya samu kanshi cikin daular da yake ganin kamar ya dauwama ke nan cikinta har Abadan Abadan.Rayuwa hakika ba tada tabbas komai yana iya faruwa kowane lokaci al’amarin haka ne duk wani al’amarin da yake, to ya kwana da sanin cewa watarana ko ya shirya ko bai shirya, haka abin zai zo ma shi.

Hausawa sun ce in ana dara fidda Uwa ake yi shi yasa aka fara da Jihar Nasarawa Jiha ce ta Shugaban jam’iyyar APC na kasa Sanata Abdullahi Adamu wanda ya wakilci mazabar majalisar Dattawa ta Nasarawa ta yamma, shi tun a mazabar shi ta unguwar GRA ta garin Keffi jam’iyyar Labour Party ta kjada shi.Bugu da kari kuma jam’iyyar SDP ta lashe kujeru biyu daga cikin uku na Dattawa da suka hada da Ahmed Aliyu daya taba zama dan majalisar wakilai ta tarayya a zamanin mulkin tsohon Shugaban kasa Olusegun Obasanjo. Zai wakilci mazabar majalisar Dattawa ta Nasarawa ta yamma.Sanata Godiya Akwashiki Nasarawa ta Arewa daga nan sai Onawo Mohammed Ogoshi na jam’iyyar PDP.Akwai dan majalisar wakilai ta tarayya da zai wakilci mazabar Keffi Karu da Kokona Gaza Jonathan daga jam’iyyar SDP, wani babban koma baya ga shi Shugaban APC shine yadda jam’iyyar LP ce ta lashe zaben Shugaban kasa.Abin ya wuce ma al’amarin majalisun kasa.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

Sanata Philip Tanimu Aduda da ke wakiltar Babban birin tarayya ya kwashe shekara da shekara ya na damawa a harkar siyasar Babban Birnin Tarayya Abuja, ya shafe shekara takwas yana dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tarayya ta kananan hukumomin Abuja da Bwari.Sai dan majalisar dattawa mai wakiltar Babban Birnin Tarayya inda shi ma sauran watanni uku ya cika shekara takwas, zaben ‘yan majalisar Dattawa da aka gabatar ranar Asabar ta makon daya gabata ne ya fafata tsakanin shi da wasu ‘yan takara biyu da suka hada da Ireti Kingibe’yar-takarar jam’iyyar LP.Ta kwashe shekaru da suka kai ashirin da uku tana gwagwarmayar siyasa inda ta fito takara Sanata karkashin jam’iyyu daban- daban, sai wannan zaben shekarar 2023 ne Allah ya bata sa’a.

Dantakarar majalisar dattawa a karkashin jam’iyyar Labour Party Mista Donatus Mathew shine wanda hukumar zabe ta bayyana ya lashe zaben kujerar majalisar Wakilai ta tarayya na mazabar Kaura ta tarayya.Kafin dai haka sai yayi sana’ar Okada, ya taba yin Kansila lokacin mulkin Makarfi amma daga baya sai al’amura suka canza ma shi. Bello Nasiru El Rufai ya samu Nasarar lashe zaben dan majalisar ta wakilai ta tarayya indazai wakilci mazabar Kaduna ta Arewa. Shi ma Sadik Ango Abdullahi wanda yana daga cikin wadanda yana daga cikin wadanda maharan Jirgin kasa mai zuwa Kaduna daga Abuja, ya lashe zaben majalisar wakilai ta Tarayya ta SabonGarin Zariya.

Sanata Bala Ibn Na Allah kafin ya zama Sanata ya fara zama dan majalisar wakilai ne ta Tarayya daga shekarar daga shekara ta 2003 zuwa 2011,sai majalisar Dattawa ta kasa daga 2015 zuwa 2023,wanda bayan an kamamla zaben ne Garba Musa Maidoki na jam’iyyar PDP wanda kuma wannan shine karon shi na farko daya fara fito takara ya kuma samu damar kada wanda ya dade yana damawa a harkokin siyasar.Sanata Bala Ibn Na Allah ajin shi daya da Sanata Philip Aduda ganin yadda suka kwashe shekaru maso yawa tsakanin majalisun Wakilai da Dattawa na kasa.

Jihar Gombe ma akwai Sanata Ibrahim Gombe ta tsakiya Dankwambo wanda tsohon gwaman Jihar Gombe ne, a shekarun da suka gabata yayi kokarin tsayawar Sanata amma abin yaci tura sai wannan lokacine.Kamar dai an yi ma shi ritaya ne ko yayi ma kanshi duk da yake dai duk al’amarin na Allah ne duk lokacin daya ba mutum lokacin ne yaga yafi dace da shi.Akwai kuma Sanata Anthony Siyako Gombe ta Arewa.

Jihar Kano kuma akwai guguwar siyasar Kwankwansiyya ta jam’iyyar NNPP wadda tayi awon gaba ta wasu shahararrun ‘yan siyasar ta Kano biyu da suka hada da Sanata Kabir Gaya mai wakiltar mazabar Kano ta Kudu da suaka hada da Sanata Kabiru Ibrahim Gaya an zabe a majalisar Dattawa ne sau uku a zabubbukan shekara ta 2007, 2011, 2015 da kuam 2019. Shi ma dan gida ne idana ana maganar majalisar kasa sai kuma a zaben shekara ta 2023 inda bai samu nasara ba lashewa ba, bayan Kawu Sumaila na jam’iyyar NNPP ya kada shi a zaben,saboda ko karamar hukumar shi ta Gaya bai ci ba.

Jihar Katsina Sanata Ahmed Babba Kaita wanda ya koma jam’iyyar PDP daga APC bai samu nasara ba saboda Alhaji Nasiru Sani Zangon Daura dan takara majalisar Dattawa na jam’iyyar APC na Katsina ta Arewa shine ya kada shi.Abdul’aziz Musa ‘Yar’aduwa kanine na tsohonShugaban kasa marigayi Umaru ‘Yar’aduwa shi ya lashen zaben mazabar majalisar Dattawa ta Katsina ta tsakiya. Sanata Ahmed Babba Kaita shi ma ya dade a majalisar kasa domin ya shafe shekaru a tsakanin majalisar Wakilai da majalisarDattawa ta kasa,amma a wannan zaben 2023 sai Allah ya ba wani. Muntari Dandutse an zabe shi a matsayin sabon Sanata mai wakiltar mazabar Katsina ta Kudu tsohon dan majalisar wakilai neta tarayya wanda har yanzu bai kai ga kammala wa’adin shi ba.

Zabar sabbin ‘yan majalisar Dattawa da wakilai na kasa a ranar 25 ga watan Fabrairu 2023 wata dama ce da suma zasu bada tasu gudunmawa wajen cigaban kasa,maimakon yadda wasu ke mamayeb ta su maida wurin kamar wani gidansu na gado.Wani sauyi ne daya zo daga Allah inda ya bada wata dama har aka kai ga zaben su sabbin ‘yan majalisun na kasa.Akwai wadanda wadansu gwamnonin da ke kammala wa’adinsu watanni uku masu zuwa, sun tsaya takara amma Allah bai yadda ba hakar tasu bata cimma ruwa ba,don haka yadda Allah ya so aka dama ta hakane za’a sha ta.

majalisar kasa
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

MASU ALAKA

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
Manyan Labarai

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa
Siyasa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026
Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci
Siyasa

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

July 8, 2026
Next Post
Bazoum Ya Taya Tinubu Murnar Lashe Zabe

Bazoum Ya Taya Tinubu Murnar Lashe Zabe

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.