ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Batun Bayyana Sakamakon Zabe Ta Na’ura A Cikin Dokar Zabe –Lawan

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Lawan

Shugaban majalisan dattawa, Ahmad Lawan ya yi ikirarin cewa tun asali babu batun bayyana sakamakon zabe ta na’urar BVAS a cikin dokar zabe ta shekarar 2022.

Lawan ya yi wannan ikirarin ne a lokacin da yake bayar da gudunmuwarsa kan kudirin da Sanata Ibrahim Oloriegbe, mai wakiltar mazabar Kwara ta tsakiya a karkashin jam’iyyar APC ya yi kan ce-ce-ku-cen da ya biyo bayan zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya na ranar 25 ga watan Fabrairu kan kin yin amfani da bayyana sakamakon zabe ta na’urar BVAS.

  • Zaben 2023: Bazatar Da Aka Samu A Majalisar Kasa

Shugaban majalisar dattawan, ya ce abin da majalisar ta amince da shi ne na tattara sakamakon zabe da kuma mika shi ga hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC).

ADVERTISEMENT

A cikin kudurin na Sanata Oloriegbe, ya bukaci majalisar dattijai ta bukaci dukkanin masu ruwa da tsaki na siyasa, shugabanni da kowane dan Nijeriya da su kwantar da hankalinsu, su bar batun maganar bayyana sakamakon zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisar dokokin kasar, bisa tanadin dokar zabe.

Sanata Sani Musa, daga Jihar Neja, ya ce tun da ‘yan Nijeriya ba su yi zabe ta hanyar bayyana sakamakon zabe ta na’ura ba, batun neman INEC ta aika da sakamakon ta hanyar lantarki bai zama dole ba, saboda dokar zabe ba ta umurci hukumar zabe ta yi hakan ba.

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Sai dai mahawarar ta haifar da ce-ce-ku-ce a tsakanin ‘yan majalisar bisa tsarin jam’iyyar, saboda sabanin ra’ayi da sanatocin PDP suka yi, inda suka bukaci a janye kudirin.

Shugaban marasa rinjaye na majalisar dattawa, Sanata Chukwuka Utazi, a lokacin da yake bayar da kudirinsa, ya bukaci hukumar zabe ta INEC da ta bi dokar zabe kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanada.

Da yake jawabi, Sanata Uche Ekwunife, jigo a jam’iyyar PDP, mai wakiltan Anambra ta tsakiya, ya dage da cewa ya kamata INEC ta bi tsarin dokar zabe.

Sanata Biodun Olujimi, wanda shi ma dan jam’iyyar adawa ta PDP ne, ya yi kira da a samar da zaman lafiya, inda ya bukaci ‘yan Nijeriya da su kwantar da hankula ta yadda za a shawo kan lamarin ba tare da jefa kasar cikin rudani ba.

Bugu da kari, Sanata Opeyemi Bamidele na jam’iyyar APC mai mulki a lokacin da yake magana kan batun, ya bukaci INEC da ta yi abin da ya dace bisa tanadin dokar zabe, inda ya yi kira ga ‘yan Nijeriya da su yi hakuri har INEC ta samu damar kammala aikin zabe gaba daya.

Ya kuma yi kira ga bangaren shari’a da su yi abin da ya dace, inda ya yi nuni da cewa matukar dai an yi abin da ya dace, za a shawo kan duk wata hargitsi wanda za ta wanzar da zaman lafiya.

Mataimakin mai tsawatarwa na majalisar dattawa, Aliyu Sabi, a nasa jawabin ya yi kira ga ‘yan Nijeriya da su bari a ci gaba da gudanar da aikin domin a karfafa dimokuradiyya.

Da yawa daga cikin ‘yan majalisar sun ba da gudunmawa, domin nuna goyon bayansu ga kudirin, wanda ya kai ga amincewa da shi, bayan da shugaban majalisar ya kada kuri’a.

A jawabinsa na rufe kudirin, Lawan ya bukaci duk wanda bai gamsu da hukuncin da INEC ta yanke ba da ya garzaya kotu, amma ka da ya kawo matsala a kasar.

Lawan
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya
Labarai

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Next Post
Mutum 25 Ne Suka Bace Cikin Wata 6 A Jihar Abia — ‘Yan Sanda

'Yansanda Sun Tabbatar Da Mutuwar Mutum 12 Yayin Tashin Bam A Wurin Hako Danyen Mai A Ribas

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.