ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Batun Bayyana Sakamakon Zabe Ta Na’ura A Cikin Dokar Zabe –Lawan

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Lawan

Shugaban majalisan dattawa, Ahmad Lawan ya yi ikirarin cewa tun asali babu batun bayyana sakamakon zabe ta na’urar BVAS a cikin dokar zabe ta shekarar 2022.

Lawan ya yi wannan ikirarin ne a lokacin da yake bayar da gudunmuwarsa kan kudirin da Sanata Ibrahim Oloriegbe, mai wakiltar mazabar Kwara ta tsakiya a karkashin jam’iyyar APC ya yi kan ce-ce-ku-cen da ya biyo bayan zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya na ranar 25 ga watan Fabrairu kan kin yin amfani da bayyana sakamakon zabe ta na’urar BVAS.

  • Zaben 2023: Bazatar Da Aka Samu A Majalisar Kasa

Shugaban majalisar dattawan, ya ce abin da majalisar ta amince da shi ne na tattara sakamakon zabe da kuma mika shi ga hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC).

ADVERTISEMENT

A cikin kudurin na Sanata Oloriegbe, ya bukaci majalisar dattijai ta bukaci dukkanin masu ruwa da tsaki na siyasa, shugabanni da kowane dan Nijeriya da su kwantar da hankalinsu, su bar batun maganar bayyana sakamakon zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisar dokokin kasar, bisa tanadin dokar zabe.

Sanata Sani Musa, daga Jihar Neja, ya ce tun da ‘yan Nijeriya ba su yi zabe ta hanyar bayyana sakamakon zabe ta na’ura ba, batun neman INEC ta aika da sakamakon ta hanyar lantarki bai zama dole ba, saboda dokar zabe ba ta umurci hukumar zabe ta yi hakan ba.

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Sai dai mahawarar ta haifar da ce-ce-ku-ce a tsakanin ‘yan majalisar bisa tsarin jam’iyyar, saboda sabanin ra’ayi da sanatocin PDP suka yi, inda suka bukaci a janye kudirin.

Shugaban marasa rinjaye na majalisar dattawa, Sanata Chukwuka Utazi, a lokacin da yake bayar da kudirinsa, ya bukaci hukumar zabe ta INEC da ta bi dokar zabe kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanada.

Da yake jawabi, Sanata Uche Ekwunife, jigo a jam’iyyar PDP, mai wakiltan Anambra ta tsakiya, ya dage da cewa ya kamata INEC ta bi tsarin dokar zabe.

Sanata Biodun Olujimi, wanda shi ma dan jam’iyyar adawa ta PDP ne, ya yi kira da a samar da zaman lafiya, inda ya bukaci ‘yan Nijeriya da su kwantar da hankula ta yadda za a shawo kan lamarin ba tare da jefa kasar cikin rudani ba.

Bugu da kari, Sanata Opeyemi Bamidele na jam’iyyar APC mai mulki a lokacin da yake magana kan batun, ya bukaci INEC da ta yi abin da ya dace bisa tanadin dokar zabe, inda ya yi kira ga ‘yan Nijeriya da su yi hakuri har INEC ta samu damar kammala aikin zabe gaba daya.

Ya kuma yi kira ga bangaren shari’a da su yi abin da ya dace, inda ya yi nuni da cewa matukar dai an yi abin da ya dace, za a shawo kan duk wata hargitsi wanda za ta wanzar da zaman lafiya.

Mataimakin mai tsawatarwa na majalisar dattawa, Aliyu Sabi, a nasa jawabin ya yi kira ga ‘yan Nijeriya da su bari a ci gaba da gudanar da aikin domin a karfafa dimokuradiyya.

Da yawa daga cikin ‘yan majalisar sun ba da gudunmawa, domin nuna goyon bayansu ga kudirin, wanda ya kai ga amincewa da shi, bayan da shugaban majalisar ya kada kuri’a.

A jawabinsa na rufe kudirin, Lawan ya bukaci duk wanda bai gamsu da hukuncin da INEC ta yanke ba da ya garzaya kotu, amma ka da ya kawo matsala a kasar.

Lawan
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Mutum 25 Ne Suka Bace Cikin Wata 6 A Jihar Abia — ‘Yan Sanda

'Yansanda Sun Tabbatar Da Mutuwar Mutum 12 Yayin Tashin Bam A Wurin Hako Danyen Mai A Ribas

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.