• English
  • Business News
Wednesday, October 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Gudu Ba Ja Da Baya Wajen Yaki Da Hauhawar Farashin Kayayyaki – CBN

by Yusuf Shuaibu
11 months ago
CBN

Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Olayemi Cardoso ya ce babu gudu babu ja da baya a yaki da hauhawar farashin kayayyaki.

Ya bayyana hakan ne lokacin da yake zantawa da manema labarai bayan taron kwamitin tsare-tsarena kudi a Abuja, Cardoso ya ce bankin zai ci gaba da tura duk wasu kayan aikin da ake da su don magance hauhawar farashin kayayyaki.

  • Man Fetur Da Ake Shigowa Ya Ragu Da Kashi 35 – CBN
  • CBN Ya Bayyana Shirin Kakaba Wa Bankuna Takunkumi

“Bari in fara cewa babban bankin ya jajirce wajen ci gaba da yaki da hauhawar farashin kayayyaki. Babu ja da baya kan hakan.

“Za mu sanya komai a cikin makamanmu don tabbatar da cewa mun sami damar inganta shi, kuma ba shakka, wannan ya hada da komawa ga manufofin kudi wanda aka saba da shi.

“Don haka, ina ganin yana da muhimmanci a bayyana hakan a gaba, babu gudu babu ja da baya kan hakan, ”in ji Cardoso

LABARAI MASU NASABA

Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta

Cardoso ya ce tasirin manufofin kudi na daukar lokaci don samar da sakamako, tare da jinkirin watanni shida zuwa tara, ko ma har zuwa shekara guda, ya danganta da matakan da aka aiwatar.

Gwamnan CBN ya yi hasashen cewa tasirin tsauraran manufofin na baya-bayan nan zai kara fitowa fili nan da kwata na farko na shekarar 2025.

“Muna sa ran ganin sakamako mafi girma a cikin kwata na farko na 2025, kuma za ku iya yin lissafin tun lokacin da muka fara karfafawa, don haka muna sa ran ganin wannan a farkon kwata na 2025,” in ji shi.

Cardoso ya kuma ce babban bankin yana aiki tare da hukumomin da abin ya shafa don magance kalubalen tsarin da ke shafar hauhawar farashin kayayyaki, kamar tabarbarewar wadatar kayayyaki da na matsalolin kayayyakin more rayuwa.

Ya kara da cewa CBN yana kuma kokarin ganin an kawar da gurbatattun da ake samu a kasuwar canji domin tabbatar da cewa ya fito da hakikanin darajar naira.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 
Labarai

Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

October 14, 2025
Kotu
Manyan Labarai

Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta

October 14, 2025
Asuu
Labarai

An Janye Wajibcin Samun Kiredit A Darasin Lissafi Ga Ɗaliban Fannin Zamantakewa Don Shiga Manyan Makarantu 

October 14, 2025
Next Post
Sin Ta Yi Tir Da Matakin Amurka Na Sayarwa Taiwan Makamai

Sin Ta Yi Tir Da Matakin Amurka Na Sayarwa Taiwan Makamai

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

October 14, 2025
Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

October 14, 2025
Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

October 14, 2025
Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

October 14, 2025
Kotu

Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta

October 14, 2025
Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

October 14, 2025
Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

October 14, 2025
Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo

Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo

October 14, 2025
Asuu

An Janye Wajibcin Samun Kiredit A Darasin Lissafi Ga Ɗaliban Fannin Zamantakewa Don Shiga Manyan Makarantu 

October 14, 2025
Al’ummun Kasashe Daban-Daban Sun Yabawa Shawarwarin Sin Dake Taimakawa Wajen Dunkulewa Don Hanzarta Ci Gaban Mata

Al’ummun Kasashe Daban-Daban Sun Yabawa Shawarwarin Sin Dake Taimakawa Wajen Dunkulewa Don Hanzarta Ci Gaban Mata

October 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.