• English
  • Business News
Monday, October 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

by Sulaiman
2 months ago
Soludo

Gwamnan jihar Anambra, Farfesa Chukwuma Charles Soludo, ya bayyana cewa ba shi da wata nadama kan goyon bayan da ya nuna a fili ga Shugaban Ƙasa, Bola Tinubu, duk da kasancewarsa a jam’iyyar adawa.

 

Soludo ya bayyana haka a ranar Talata yayin da yake zantawa da manema labarai a fadar shugaban ƙasa bayan wata ganawa da Tinubu a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

  • Gwamnatin Kano Za Ta Horar Da Tubabbun ‘Yandaba 718 Sana’o’i 
  • ’Yan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 6 A Taraba

Ya bayyana ganawar a matsayin mai ciki da daɗi, ya kuma ya yaba da yanayin lafiyar Shugaba Tinubu. “Shugaban Ƙasa yana cikin ƙoshin lafiya da kuzari, kuma na ji daɗin ganawa da shi. Lallai ganawa ce mai matuƙar daɗi da farinciki,” in ji Soludo.

 

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Alburusai 400 A Delta

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

Da aka tambaye shi dalilin da ya sa ya fito ƙarara ya goyi bayan shugaban ƙasa wanda ba a cikin jam’iyyarsu yake, Soludo ya ce goyon bayansa ga Tinubu ba sabon abu ba ne.

 

“An samar da waɗannan huluna tun lokacin da Shugaban Ƙasa ya ziyarci Jihar Anambra kuma kun ga allunan talla da sauran abubuwa da ke bayyana cewa masu ra’ayin kowa ci gaba suna aiki tare ne da juna,” in ji Soludo.

 

“Bayan haka, wannan wata babbar manufa ce da na yi imani da ita sosai, cewa ya kamata dukkan jam’iyyun siyasa da ke ikirarin ra’ayin ci gaba su haɗu a ƙarƙashin wata babbar ƙawance don zurfafa tunani da kawo ci gaba ba kawai a tafarkin dimokuradiyyarmu ba, har ma da ci gaban tattalin arziki da zamantakewar kasarmu.”

 

Gwamnan ya jaddada cewa kiransa na ganin masu ra’ayin ci gaba sun yi aiki tare ya samo asali ne daga yaƙini da kuma daɗaɗɗiyar alaƙar da ke tsakaninsa da Shugaban Ƙasa.

 

“Idan na ce masu ra’ayin ci gaba su yi aiki tare, kira ne ga duk masu magana kan Shugaba Bola Ahmed Tinubu… Ina nufin, ba ni da wani uzuri game da hakan.

 

“Shugaba Tinubu abokina ne, abokina ne tun shekaru 22 da suka gabata zuwa yanzu.

 

“Abokina ne, ina goyon bayansa, kuma na gamsu da matakan da ya ɗauka, musamman a fannin tattalin arziki, kuma na bayyana hakan ba sau ɗaya ba, muna kan hanyar ƙwarai kuma muna buƙatar mu ci gaba a haka,” in ji Soludo.

 

Game da halin tsaro a Jihar Anambra, gwamnan ya ce gwamnatinsa ta ɗauki wani tsari na bai-daya tun daga watan Janairu, biyo bayan zartar da dokar tsaron cikin gida a jihar.

 

“Ana kokarin tunkarar matsalar rashin tsaro ne tun daga tushe. Dukkanin miyagun ‘yan ta’adda sun tsere daga jihar saboda su ne ke yaudarar matasanmu da kuma jefa su cikin aikata laifuka,” in ji shi.

 

Soludo ya ce gwamnati na amfani da matakan karfi da na lallashi don magance matsalar rashin tsaro.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Alburusai 400 A Delta

October 20, 2025
Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC
Labarai

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

October 19, 2025
Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi
Manyan Labarai

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

October 19, 2025
Next Post
EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam'iyar ADC Ta Yi

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kama Alburusai 400 A Delta

October 20, 2025
Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

October 19, 2025
Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

October 19, 2025
Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

October 19, 2025
Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

October 19, 2025
Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

October 19, 2025
Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

October 19, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

October 19, 2025
Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

October 19, 2025
Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

October 19, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.