• English
  • Business News
Tuesday, October 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Wata Kasa Da Za Ta Tsira Muddin Akasarin Kasashen Duniya Na Cikin Tashin Hankali 

by CGTN Hausa
2 years ago
Kasashen duniya

Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya yi kira da a yi kokarin kaucewa ra’ayin tafka asara, yayin da yake karin haske kan rahoton shekara-shekara da aka fitar gabanin kammala taron tsaro na Munich, wanda ya bayyana damuwa kan karuwar ra’ayin tabka asara. 

A yayin da ake fuskantar karuwar tabarbarewar al’amuran duniya da suka haifar da kuncin rayuwa ga tarin al’ummomi, har yanzu wasu kasashe sun fi mayar da hankali kan rungumar ra’ayin cin riba daga faduwar wata kasa. Abun da har yanzu wasu kasashe suka gaza fahimta shi ne, babu wata kasa da za ta samu kwanciyar hankali muddun akasarin kasashen duniya na fama da tashin hankali ko rashin tsaro ko talauci.

  • Ya Kamata Kasashen Yamma Su Ji Shawarwarin Kasar Sin Maimakon “Damuwa Da Asara”
  • Wang Yi Ya Yi Tir Da Karairayin Da Ake Yi Game Da Xinjiang A Munich

Abun kunya ne da takaici, a ce manyan kasashe sun zama masu cin riba daga asarar kananan kasashe maimakon zama abun dogaro ko wadanda ke tallafawa domin ganin ci gaban kasashen dake musu kallon ababen koyi.

Kamar yadda Wang Yi ya bayyana, bangaren kasar Sin ya yi imanin cewa, ra’ayin cin moriya da faduwar wani, da neman mayar da wasu saniyar ware, da yunkurin yin fito-na-fito na wani gungu, su ne ke haifar da ra’ayin “tabka hasara”.

To ina mafita?

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Ghana Da Firaministar Mozambique

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

Kamar dai yadda kullum kasar Sin ke kira, mafitar ita ce tabbatar da daidaito tsakanin kasa da kasa ta hanyar inganta hulda da cudanya a tsakaninsu bisa gaskiya da adalci. Idan dai za a kyautata hulda bisa gaskiya da sanin ya kamata, to tabbas babu wani bangare da zai so ganin faduwar abokan huldarsa. Ya kamata a hada karfi da karfe don a gudu tare a tsira tare.

Yanayin da duniya ta shiga, ko in ce wasu tsirarun kasashe suka jefa duniya ciki, ta shaida cewa, idan har ba a dawo kan turbar da ta dace ta daidaito da adalci ba, to ba za a samu kyakkyawar makomar da ake buri ba.

Kasar Sin mai rajin ganin an samu ci gaba da tabbatuwar adalci da cudanya da hadin gwiwar bangarori daban daban, ita kadai ba za ta iya tabbatar da hakan ba. Dole manyan kasashe su mara mata baya, su ba da gudunmawarsu bil hakki da gaskiya, su ajiye girman kai da hadama, a hada hannu a ceto duniya daga durkushewa. (Fa’iza Mustapha)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Ghana Da Firaministar Mozambique
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Ghana Da Firaministar Mozambique

October 14, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

October 13, 2025
Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta
Daga Birnin Sin

Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

October 13, 2025
Next Post
Kwastam Za Ta Raraba Wa ‘Yan Nijeriya Shinkafa Da Sauran Kayan Da Ta Kwato

Kwastam Za Ta Raraba Wa 'Yan Nijeriya Shinkafa Da Sauran Kayan Da Ta Kwato

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Wakilai Ta Buƙaci Hukumomin Tsaro Su Kai Agajin Gaggawa A Sakkwato

Majalisar Wakilai Ta Buƙaci Hukumomin Tsaro Su Kai Agajin Gaggawa A Sakkwato

October 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Ghana Da Firaministar Mozambique

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Ghana Da Firaministar Mozambique

October 14, 2025
‘Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP

PDP Ta Ɗage Babban Taronta Biyo Bayan Ficewar Wasu Manyan Jiga-jigai

October 14, 2025
An Kashe Mutum 3, Wasu 7 Sun Jikkata Sakamakon Ɓarkewar Rikici A Jihar Jigawa

An Kashe Mutum 3, Wasu 7 Sun Jikkata Sakamakon Ɓarkewar Rikici A Jihar Jigawa

October 14, 2025
Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi

Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi

October 14, 2025
Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

October 14, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Jarida A Kan Hanyarsa Ta Zuwa Ɗaukar Horo A Kwara

‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Jarida A Kan Hanyarsa Ta Zuwa Ɗaukar Horo A Kwara

October 14, 2025
Zaman Gidan Yari Ya Nuna Min Mutanen Da Ya Kamata Na Yi Hulɗar Siyasa Da Su — Faruk Lawan

Zaman Gidan Yari Ya Nuna Min Mutanen Da Ya Kamata Na Yi Hulɗar Siyasa Da Su — Faruk Lawan

October 14, 2025
Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026

Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026

October 13, 2025
Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

October 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.