• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Wata Kasa Da Za Ta Tsira Muddin Akasarin Kasashen Duniya Na Cikin Tashin Hankali 

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Babu Wata Kasa Da Za Ta Tsira Muddin Akasarin Kasashen Duniya Na Cikin Tashin Hankali 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya yi kira da a yi kokarin kaucewa ra’ayin tafka asara, yayin da yake karin haske kan rahoton shekara-shekara da aka fitar gabanin kammala taron tsaro na Munich, wanda ya bayyana damuwa kan karuwar ra’ayin tabka asara. 

A yayin da ake fuskantar karuwar tabarbarewar al’amuran duniya da suka haifar da kuncin rayuwa ga tarin al’ummomi, har yanzu wasu kasashe sun fi mayar da hankali kan rungumar ra’ayin cin riba daga faduwar wata kasa. Abun da har yanzu wasu kasashe suka gaza fahimta shi ne, babu wata kasa da za ta samu kwanciyar hankali muddun akasarin kasashen duniya na fama da tashin hankali ko rashin tsaro ko talauci.

  • Ya Kamata Kasashen Yamma Su Ji Shawarwarin Kasar Sin Maimakon “Damuwa Da Asara”
  • Wang Yi Ya Yi Tir Da Karairayin Da Ake Yi Game Da Xinjiang A Munich

Abun kunya ne da takaici, a ce manyan kasashe sun zama masu cin riba daga asarar kananan kasashe maimakon zama abun dogaro ko wadanda ke tallafawa domin ganin ci gaban kasashen dake musu kallon ababen koyi.

Kamar yadda Wang Yi ya bayyana, bangaren kasar Sin ya yi imanin cewa, ra’ayin cin moriya da faduwar wani, da neman mayar da wasu saniyar ware, da yunkurin yin fito-na-fito na wani gungu, su ne ke haifar da ra’ayin “tabka hasara”.

To ina mafita?

Labarai Masu Nasaba

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Kamar dai yadda kullum kasar Sin ke kira, mafitar ita ce tabbatar da daidaito tsakanin kasa da kasa ta hanyar inganta hulda da cudanya a tsakaninsu bisa gaskiya da adalci. Idan dai za a kyautata hulda bisa gaskiya da sanin ya kamata, to tabbas babu wani bangare da zai so ganin faduwar abokan huldarsa. Ya kamata a hada karfi da karfe don a gudu tare a tsira tare.

Yanayin da duniya ta shiga, ko in ce wasu tsirarun kasashe suka jefa duniya ciki, ta shaida cewa, idan har ba a dawo kan turbar da ta dace ta daidaito da adalci ba, to ba za a samu kyakkyawar makomar da ake buri ba.

Kasar Sin mai rajin ganin an samu ci gaba da tabbatuwar adalci da cudanya da hadin gwiwar bangarori daban daban, ita kadai ba za ta iya tabbatar da hakan ba. Dole manyan kasashe su mara mata baya, su ba da gudunmawarsu bil hakki da gaskiya, su ajiye girman kai da hadama, a hada hannu a ceto duniya daga durkushewa. (Fa’iza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Don Tabbatar Da Adalci A Duniya Ana Bukatar Hadin Gwiwar “Global South”

Next Post

Kwastam Za Ta Raraba Wa ‘Yan Nijeriya Shinkafa Da Sauran Kayan Da Ta Kwato

Related

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

4 hours ago
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka
Daga Birnin Sin

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

5 hours ago
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya
Daga Birnin Sin

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

6 hours ago
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14
Daga Birnin Sin

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

7 hours ago
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

8 hours ago
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar
Daga Birnin Sin

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

10 hours ago
Next Post
Kwastam Za Ta Raraba Wa ‘Yan Nijeriya Shinkafa Da Sauran Kayan Da Ta Kwato

Kwastam Za Ta Raraba Wa 'Yan Nijeriya Shinkafa Da Sauran Kayan Da Ta Kwato

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.