ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Wata Kasa Da Za Ta Tsira Muddin Akasarin Kasashen Duniya Na Cikin Tashin Hankali 

by CGTN Hausa
2 years ago
Kasashen duniya

Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya yi kira da a yi kokarin kaucewa ra’ayin tafka asara, yayin da yake karin haske kan rahoton shekara-shekara da aka fitar gabanin kammala taron tsaro na Munich, wanda ya bayyana damuwa kan karuwar ra’ayin tabka asara. 

A yayin da ake fuskantar karuwar tabarbarewar al’amuran duniya da suka haifar da kuncin rayuwa ga tarin al’ummomi, har yanzu wasu kasashe sun fi mayar da hankali kan rungumar ra’ayin cin riba daga faduwar wata kasa. Abun da har yanzu wasu kasashe suka gaza fahimta shi ne, babu wata kasa da za ta samu kwanciyar hankali muddun akasarin kasashen duniya na fama da tashin hankali ko rashin tsaro ko talauci.

  • Ya Kamata Kasashen Yamma Su Ji Shawarwarin Kasar Sin Maimakon “Damuwa Da Asara”
  • Wang Yi Ya Yi Tir Da Karairayin Da Ake Yi Game Da Xinjiang A Munich

Abun kunya ne da takaici, a ce manyan kasashe sun zama masu cin riba daga asarar kananan kasashe maimakon zama abun dogaro ko wadanda ke tallafawa domin ganin ci gaban kasashen dake musu kallon ababen koyi.

ADVERTISEMENT

Kamar yadda Wang Yi ya bayyana, bangaren kasar Sin ya yi imanin cewa, ra’ayin cin moriya da faduwar wani, da neman mayar da wasu saniyar ware, da yunkurin yin fito-na-fito na wani gungu, su ne ke haifar da ra’ayin “tabka hasara”.

To ina mafita?

LABARAI MASU NASABA

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Kamar dai yadda kullum kasar Sin ke kira, mafitar ita ce tabbatar da daidaito tsakanin kasa da kasa ta hanyar inganta hulda da cudanya a tsakaninsu bisa gaskiya da adalci. Idan dai za a kyautata hulda bisa gaskiya da sanin ya kamata, to tabbas babu wani bangare da zai so ganin faduwar abokan huldarsa. Ya kamata a hada karfi da karfe don a gudu tare a tsira tare.

Yanayin da duniya ta shiga, ko in ce wasu tsirarun kasashe suka jefa duniya ciki, ta shaida cewa, idan har ba a dawo kan turbar da ta dace ta daidaito da adalci ba, to ba za a samu kyakkyawar makomar da ake buri ba.

Kasar Sin mai rajin ganin an samu ci gaba da tabbatuwar adalci da cudanya da hadin gwiwar bangarori daban daban, ita kadai ba za ta iya tabbatar da hakan ba. Dole manyan kasashe su mara mata baya, su ba da gudunmawarsu bil hakki da gaskiya, su ajiye girman kai da hadama, a hada hannu a ceto duniya daga durkushewa. (Fa’iza Mustapha)

Kasashen duniya
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

MASU ALAKA

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026
Daga Birnin Sin

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara
Daga Birnin Sin

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
Daga Birnin Sin

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Next Post
Kwastam Za Ta Raraba Wa ‘Yan Nijeriya Shinkafa Da Sauran Kayan Da Ta Kwato

Kwastam Za Ta Raraba Wa 'Yan Nijeriya Shinkafa Da Sauran Kayan Da Ta Kwato

LABARAI MASU NASABA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.