• English
  • Business News
Saturday, June 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Badakalar Tashar Lantarkin Mambilla: Buhari Da Obasanjo Sun Ba Da Shaida A Kotun Duniya

by Rabi'u Ali Indabawa
5 months ago
in Manyan Labarai
0
Badakalar Tashar Lantarkin Mambilla: Buhari Da Obasanjo Sun Ba Da Shaida A Kotun Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Alhamis ce Tsohon Shugaban Kasar Nijeriya Muhammadu Buhari zai gurfana a gaban kotun duniya (ICC) a Birnin Paris bisa zarginsa da hannu wajen badakalar kwangilar aikin samar da wutar lantarki ta Mambilla.

Wani kamfanin samar da wutar lantarki mai suna ‘Sunrise Power’, ya shigar da karar gwamnatin tarayya kan Dalar Amurka biliyan 2.3 bisa zargin cewa Nijeriya ta gaza cika alkawurran da ta kulla da kamfanin.

  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin: Babu Wanda Zai Ci Nasara A Yakin Cinikayya Ko Yakin Harajin Kwastam
  • Shirin Tallafinmu Ga Nijeriya A 2025 Zai Kai Ga Asalin Mabukata – Wakilin MDD

Wata majiya mai tushe da ta zanta da LEADERSHIP, ta tabbatar da faruwar lamarin. “Eh, tsohon shugaban kasar zai ba da bayanai ranar Alhamis a Faransa kan lamarin,” in ji majiyar.

Lamarin dai ya shafi ikirarin da kamfanin Sunrise Power ya yi dangane da yarjejeniyar gina tashar samar da wutar lantarki ta Mambilla mai karfin megawatt 3,050 a jihar Taraba a shekarar 2003, wanda darajarsa ta kai Dala biliyan 6.

Kamfanin dai ya yi zargin cewa gwamnatin tarayya ta gaza cika alkawurran kwangilar da ta rataya a wuyanta, wanda ya kai ga yin shari’a a kotun ICC.

Labarai Masu Nasaba

Wanda Ya Yi Gangancin Taba Takarar Shettima Ya Gayyato Wa APC Faɗuwa A 2027 – Aminu Boyi 

Duk Da Jihohin Nijeriya Sun Fara Biyan Mafi Ƙarancin Albashi Na 70,000, Ana Ci Gaba Da Fuskantar Matsin Rayuwa

A halin da ake ciki kuma, fadar shugaban kasa ta yi watsi da rahotannin kafafen sada zumunta na baya-bayan nan da ke nuni da cewa Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya tursasa manyan ‘yan Nijeriya da su shiga tsakani.

A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar, mai ba Shugaban Kasa Shawara a Harkokin Yada Labarai da Dabaru, Bayo Onanuga, ya bayyana ikirarin a matsayin “Karya da yaudara.”

“Tsarin sasantawa ya kasance sirri ne, kuma wadanda ke da hannu a cikin tsaron Nijeriya suna yin haka ne bisa radin kansu, saboda kishin kasa da kuma jin dadin aiki,” in ji Onanuga. “Babu inda shugaba Tinubu ya matsa wa wani ya shaida ko kuma ya hana kowa yin hakan.”

Wani kamfanin wutar lantarki mai suna Sunrise Power, ya fara gudanar da shari’ar a ranar 10 ga Oktoba, 2017, inda ya nemi diyyar Dala biliyan 2.354 kan abin da ya bayyana a matsayin karya yarjejeniyar kwangila.

Kamfanin ya yi ikirarin cewa gwamnatin tarayya ta karya yarjejeniyar 2003 na aikin Mambilla, wanda aka kirkira da farko a matsayin tsarin “gina, aiki, da canja wuri”

A shekarar 2017, ministan wutar lantarki, ayyuka da gidaje na lokacin Babatunde Fashola ya bayyana Sunrise Power a matsayin “mai tsaka-tsaki,” inda ya bayyana cewa gwamnatin Buhari ta dauki kamfanin Sinohydro Corporation Limited, wani kamfani na kasar China, a matsayin dan kwangilar aikin Injiniya, saye da gine-gine (EPC). .

Sai dai yayin da aka ce an amince da yarjejeniyar ta Dala miliyan 200 a shekarar 2020, daga baya Sunrise Power ta shigar da sabuwar kara kan Dala miliyan 400 a kotun ICC, tana mai zargin gwamnati da kin cika sharudan sasantawa. Har ila yau, kamfanin ya nemi a maido da shi a matsayin abokin hulda na aikin Mambilla na Dala biliyan 5.8 da aka sakewa fasali, a cewarsa an cire shi a tattaunawar da ta biyo baya.

Wakilin Lauyoyin Sunrise, Femi Falana ne ya shigar da karar a kotun ta ICC, inda ya bukaci gwamnati ta biya diyyar Dala miliyan 400 da kuma tarar da ta saba wa yarjejeniyar. Bukatar hakan ta kunshi hukuncin ba da kashi 10 cikin 100 na jinkiri fiye da kayyadaddun lokutan sasantawa na kwanaki 14 da aka amince da su a cikin Janairu 2020.

Gwamnatin tarayya ta bayar da hujjar cewa an sake duba sharudan yarjejeniyar ne saboda matsalar kudi da annobar Korona ta haifar, wanda ya haifar da sabuwar tattaunawa.

Sakamakon sulhun na iya yin tasiri sosai ga harkokin kudi na Nijeriya da kuma makomar aikin wutar lantarki na Mambilla da aka dade ana jan kafa.

A halin yanzu dai Tsohon Shugaban Kasa Olusegun Obasanjo yana Birnin Paris don karrama goron gayyatar da aka yi masa na yin jawabi kan aikin samar da wutar lantarkin Mambila.

LEADERSHIP ta nakalto cewa tsohon shugaban ya bar Nijeriya zuwa Birnin Paris a safiyar ranar Asabar domin samun damar bayyana ya kuma yi magana a kan lamarin, wanda zai iya ci gaba da tafiya kamar yadda muke magana.

Mataimaki na musamman ga Obasanjo kan harkokin yada labarai, Kehinde Akin Yemi, ya tabbatar wa LEADERSHIP a ranar Litinin da yamma a Abeokuta cewa Obasanjo ya zabi girmama gayyatar ne domin daidaita al’amura.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuhariMambilaObasanjo
ShareTweetSendShare
Previous Post

Karrama Sojojinmu Da Suka Sadaukar Da Kai Don Ɗorewar Nijeriya

Next Post

Yadda Ficewar Kwararrun Ma’aikata Daga Nijeriya Ke Barazana Ga Tattalin Arzikin Kasa

Related

Wanda Ya Yi Gangancin Taba Takarar Shettima Ya Gayyato Wa APC Faɗuwa A 2027 – Aminu Boyi 
Manyan Labarai

Wanda Ya Yi Gangancin Taba Takarar Shettima Ya Gayyato Wa APC Faɗuwa A 2027 – Aminu Boyi 

40 minutes ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Manyan Labarai

Duk Da Jihohin Nijeriya Sun Fara Biyan Mafi Ƙarancin Albashi Na 70,000, Ana Ci Gaba Da Fuskantar Matsin Rayuwa

3 hours ago
Atiku Da Wasu Sun Kafa Sabuwar Jam’iyya, Sun Nemi INEC Ta Musu Rajista
Manyan Labarai

Atiku Da Wasu Sun Kafa Sabuwar Jam’iyya, Sun Nemi INEC Ta Musu Rajista

13 hours ago
Ba Tsoro Ne Yasa Muka Amince Da Sulhu Da Ƴan Bindiga Ba – Gwamnatin Sokoto
Manyan Labarai

Ba Tsoro Ne Yasa Muka Amince Da Sulhu Da Ƴan Bindiga Ba – Gwamnatin Sokoto

18 hours ago
Tinubu Zai Zaɓi Mataimakinsa Bayan Taron Jam’iyya – Fadar Shugaban Ƙasa 
Manyan Labarai

Tinubu Zai Zaɓi Mataimakinsa Bayan Taron Jam’iyya – Fadar Shugaban Ƙasa 

22 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Filato, Mutane 15 Sun Mutu A Bokkos Da Mangu
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Filato, Mutane 15 Sun Mutu A Bokkos Da Mangu

23 hours ago
Next Post
Yadda Ficewar Kwararrun Ma’aikata Daga Nijeriya Ke Barazana Ga Tattalin Arzikin Kasa

Yadda Ficewar Kwararrun Ma’aikata Daga Nijeriya Ke Barazana Ga Tattalin Arzikin Kasa

LABARAI MASU NASABA

Wanda Ya Yi Gangancin Taba Takarar Shettima Ya Gayyato Wa APC Faɗuwa A 2027 – Aminu Boyi 

Wanda Ya Yi Gangancin Taba Takarar Shettima Ya Gayyato Wa APC Faɗuwa A 2027 – Aminu Boyi 

June 21, 2025
Iran Ta Bayyana Sharaɗin Sasantawa Da Isra’ila – Ministan Harkokin Waje

Iran Ta Bayyana Sharaɗin Sasantawa Da Isra’ila – Ministan Harkokin Waje

June 21, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)

Duk Da Jihohin Nijeriya Sun Fara Biyan Mafi Ƙarancin Albashi Na 70,000, Ana Ci Gaba Da Fuskantar Matsin Rayuwa

June 21, 2025
Rundunar PLA Ta Soki Birtaniya Bisa Zuzuta Abun Da Ya Wakana Yayin Da Jirgin Ruwan Sintirinta Ya Keta Ta Zirin Taiwan 

Rundunar PLA Ta Soki Birtaniya Bisa Zuzuta Abun Da Ya Wakana Yayin Da Jirgin Ruwan Sintirinta Ya Keta Ta Zirin Taiwan 

June 20, 2025
Hadin Gwiwa Da Sin Na Bunkasa Zaman Lafiya Da Daidaito A Yankin Kahon Afirka

Hadin Gwiwa Da Sin Na Bunkasa Zaman Lafiya Da Daidaito A Yankin Kahon Afirka

June 20, 2025
Me Ya Kamata Mai Yaron Ciki Ta Kula Da Shi?

Me Ya Kamata Mai Yaron Ciki Ta Kula Da Shi?

June 20, 2025
Atiku Da Wasu Sun Kafa Sabuwar Jam’iyya, Sun Nemi INEC Ta Musu Rajista

Atiku Da Wasu Sun Kafa Sabuwar Jam’iyya, Sun Nemi INEC Ta Musu Rajista

June 20, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)

June 20, 2025
Sin Ta Jadadda Wajibcin Daukar Jerin Matakan Magance Matsalar Talauci Da Karancin Ci Gaba Da Rikici

Sin Ta Jadadda Wajibcin Daukar Jerin Matakan Magance Matsalar Talauci Da Karancin Ci Gaba Da Rikici

June 20, 2025
Jakadan Sin Dake Amurka Ya Yi Jawabi A Gun Liyafar Da Kwamitin Kasa Mai Lura Da Kasuwancin Amurka Da Sin Ya Shirya

Jakadan Sin Dake Amurka Ya Yi Jawabi A Gun Liyafar Da Kwamitin Kasa Mai Lura Da Kasuwancin Amurka Da Sin Ya Shirya

June 20, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.