ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Badakalar Tashar Lantarkin Mambilla: Buhari Da Obasanjo Sun Ba Da Shaida A Kotun Duniya

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
Mambilla

A ranar Alhamis ce Tsohon Shugaban Kasar Nijeriya Muhammadu Buhari zai gurfana a gaban kotun duniya (ICC) a Birnin Paris bisa zarginsa da hannu wajen badakalar kwangilar aikin samar da wutar lantarki ta Mambilla.

Wani kamfanin samar da wutar lantarki mai suna ‘Sunrise Power’, ya shigar da karar gwamnatin tarayya kan Dalar Amurka biliyan 2.3 bisa zargin cewa Nijeriya ta gaza cika alkawurran da ta kulla da kamfanin.

  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin: Babu Wanda Zai Ci Nasara A Yakin Cinikayya Ko Yakin Harajin Kwastam
  • Shirin Tallafinmu Ga Nijeriya A 2025 Zai Kai Ga Asalin Mabukata – Wakilin MDD

Wata majiya mai tushe da ta zanta da LEADERSHIP, ta tabbatar da faruwar lamarin. “Eh, tsohon shugaban kasar zai ba da bayanai ranar Alhamis a Faransa kan lamarin,” in ji majiyar.

ADVERTISEMENT

Lamarin dai ya shafi ikirarin da kamfanin Sunrise Power ya yi dangane da yarjejeniyar gina tashar samar da wutar lantarki ta Mambilla mai karfin megawatt 3,050 a jihar Taraba a shekarar 2003, wanda darajarsa ta kai Dala biliyan 6.

Kamfanin dai ya yi zargin cewa gwamnatin tarayya ta gaza cika alkawurran kwangilar da ta rataya a wuyanta, wanda ya kai ga yin shari’a a kotun ICC.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

A halin da ake ciki kuma, fadar shugaban kasa ta yi watsi da rahotannin kafafen sada zumunta na baya-bayan nan da ke nuni da cewa Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya tursasa manyan ‘yan Nijeriya da su shiga tsakani.

A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar, mai ba Shugaban Kasa Shawara a Harkokin Yada Labarai da Dabaru, Bayo Onanuga, ya bayyana ikirarin a matsayin “Karya da yaudara.”

“Tsarin sasantawa ya kasance sirri ne, kuma wadanda ke da hannu a cikin tsaron Nijeriya suna yin haka ne bisa radin kansu, saboda kishin kasa da kuma jin dadin aiki,” in ji Onanuga. “Babu inda shugaba Tinubu ya matsa wa wani ya shaida ko kuma ya hana kowa yin hakan.”

Wani kamfanin wutar lantarki mai suna Sunrise Power, ya fara gudanar da shari’ar a ranar 10 ga Oktoba, 2017, inda ya nemi diyyar Dala biliyan 2.354 kan abin da ya bayyana a matsayin karya yarjejeniyar kwangila.

Kamfanin ya yi ikirarin cewa gwamnatin tarayya ta karya yarjejeniyar 2003 na aikin Mambilla, wanda aka kirkira da farko a matsayin tsarin “gina, aiki, da canja wuri”

A shekarar 2017, ministan wutar lantarki, ayyuka da gidaje na lokacin Babatunde Fashola ya bayyana Sunrise Power a matsayin “mai tsaka-tsaki,” inda ya bayyana cewa gwamnatin Buhari ta dauki kamfanin Sinohydro Corporation Limited, wani kamfani na kasar China, a matsayin dan kwangilar aikin Injiniya, saye da gine-gine (EPC). .

Sai dai yayin da aka ce an amince da yarjejeniyar ta Dala miliyan 200 a shekarar 2020, daga baya Sunrise Power ta shigar da sabuwar kara kan Dala miliyan 400 a kotun ICC, tana mai zargin gwamnati da kin cika sharudan sasantawa. Har ila yau, kamfanin ya nemi a maido da shi a matsayin abokin hulda na aikin Mambilla na Dala biliyan 5.8 da aka sakewa fasali, a cewarsa an cire shi a tattaunawar da ta biyo baya.

Wakilin Lauyoyin Sunrise, Femi Falana ne ya shigar da karar a kotun ta ICC, inda ya bukaci gwamnati ta biya diyyar Dala miliyan 400 da kuma tarar da ta saba wa yarjejeniyar. Bukatar hakan ta kunshi hukuncin ba da kashi 10 cikin 100 na jinkiri fiye da kayyadaddun lokutan sasantawa na kwanaki 14 da aka amince da su a cikin Janairu 2020.

Gwamnatin tarayya ta bayar da hujjar cewa an sake duba sharudan yarjejeniyar ne saboda matsalar kudi da annobar Korona ta haifar, wanda ya haifar da sabuwar tattaunawa.

Sakamakon sulhun na iya yin tasiri sosai ga harkokin kudi na Nijeriya da kuma makomar aikin wutar lantarki na Mambilla da aka dade ana jan kafa.

A halin yanzu dai Tsohon Shugaban Kasa Olusegun Obasanjo yana Birnin Paris don karrama goron gayyatar da aka yi masa na yin jawabi kan aikin samar da wutar lantarkin Mambila.

LEADERSHIP ta nakalto cewa tsohon shugaban ya bar Nijeriya zuwa Birnin Paris a safiyar ranar Asabar domin samun damar bayyana ya kuma yi magana a kan lamarin, wanda zai iya ci gaba da tafiya kamar yadda muke magana.

Mataimaki na musamman ga Obasanjo kan harkokin yada labarai, Kehinde Akin Yemi, ya tabbatar wa LEADERSHIP a ranar Litinin da yamma a Abeokuta cewa Obasanjo ya zabi girmama gayyatar ne domin daidaita al’amura.

Mambilla
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Yadda Ficewar Kwararrun Ma’aikata Daga Nijeriya Ke Barazana Ga Tattalin Arzikin Kasa

Yadda Ficewar Kwararrun Ma’aikata Daga Nijeriya Ke Barazana Ga Tattalin Arzikin Kasa

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.