ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Badakalar Tashar Lantarkin Mambilla: Buhari Da Obasanjo Sun Ba Da Shaida A Kotun Duniya

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
Mambilla

A ranar Alhamis ce Tsohon Shugaban Kasar Nijeriya Muhammadu Buhari zai gurfana a gaban kotun duniya (ICC) a Birnin Paris bisa zarginsa da hannu wajen badakalar kwangilar aikin samar da wutar lantarki ta Mambilla.

Wani kamfanin samar da wutar lantarki mai suna ‘Sunrise Power’, ya shigar da karar gwamnatin tarayya kan Dalar Amurka biliyan 2.3 bisa zargin cewa Nijeriya ta gaza cika alkawurran da ta kulla da kamfanin.

  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin: Babu Wanda Zai Ci Nasara A Yakin Cinikayya Ko Yakin Harajin Kwastam
  • Shirin Tallafinmu Ga Nijeriya A 2025 Zai Kai Ga Asalin Mabukata – Wakilin MDD

Wata majiya mai tushe da ta zanta da LEADERSHIP, ta tabbatar da faruwar lamarin. “Eh, tsohon shugaban kasar zai ba da bayanai ranar Alhamis a Faransa kan lamarin,” in ji majiyar.

ADVERTISEMENT

Lamarin dai ya shafi ikirarin da kamfanin Sunrise Power ya yi dangane da yarjejeniyar gina tashar samar da wutar lantarki ta Mambilla mai karfin megawatt 3,050 a jihar Taraba a shekarar 2003, wanda darajarsa ta kai Dala biliyan 6.

Kamfanin dai ya yi zargin cewa gwamnatin tarayya ta gaza cika alkawurran kwangilar da ta rataya a wuyanta, wanda ya kai ga yin shari’a a kotun ICC.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

A halin da ake ciki kuma, fadar shugaban kasa ta yi watsi da rahotannin kafafen sada zumunta na baya-bayan nan da ke nuni da cewa Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya tursasa manyan ‘yan Nijeriya da su shiga tsakani.

A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar, mai ba Shugaban Kasa Shawara a Harkokin Yada Labarai da Dabaru, Bayo Onanuga, ya bayyana ikirarin a matsayin “Karya da yaudara.”

“Tsarin sasantawa ya kasance sirri ne, kuma wadanda ke da hannu a cikin tsaron Nijeriya suna yin haka ne bisa radin kansu, saboda kishin kasa da kuma jin dadin aiki,” in ji Onanuga. “Babu inda shugaba Tinubu ya matsa wa wani ya shaida ko kuma ya hana kowa yin hakan.”

Wani kamfanin wutar lantarki mai suna Sunrise Power, ya fara gudanar da shari’ar a ranar 10 ga Oktoba, 2017, inda ya nemi diyyar Dala biliyan 2.354 kan abin da ya bayyana a matsayin karya yarjejeniyar kwangila.

Kamfanin ya yi ikirarin cewa gwamnatin tarayya ta karya yarjejeniyar 2003 na aikin Mambilla, wanda aka kirkira da farko a matsayin tsarin “gina, aiki, da canja wuri”

A shekarar 2017, ministan wutar lantarki, ayyuka da gidaje na lokacin Babatunde Fashola ya bayyana Sunrise Power a matsayin “mai tsaka-tsaki,” inda ya bayyana cewa gwamnatin Buhari ta dauki kamfanin Sinohydro Corporation Limited, wani kamfani na kasar China, a matsayin dan kwangilar aikin Injiniya, saye da gine-gine (EPC). .

Sai dai yayin da aka ce an amince da yarjejeniyar ta Dala miliyan 200 a shekarar 2020, daga baya Sunrise Power ta shigar da sabuwar kara kan Dala miliyan 400 a kotun ICC, tana mai zargin gwamnati da kin cika sharudan sasantawa. Har ila yau, kamfanin ya nemi a maido da shi a matsayin abokin hulda na aikin Mambilla na Dala biliyan 5.8 da aka sakewa fasali, a cewarsa an cire shi a tattaunawar da ta biyo baya.

Wakilin Lauyoyin Sunrise, Femi Falana ne ya shigar da karar a kotun ta ICC, inda ya bukaci gwamnati ta biya diyyar Dala miliyan 400 da kuma tarar da ta saba wa yarjejeniyar. Bukatar hakan ta kunshi hukuncin ba da kashi 10 cikin 100 na jinkiri fiye da kayyadaddun lokutan sasantawa na kwanaki 14 da aka amince da su a cikin Janairu 2020.

Gwamnatin tarayya ta bayar da hujjar cewa an sake duba sharudan yarjejeniyar ne saboda matsalar kudi da annobar Korona ta haifar, wanda ya haifar da sabuwar tattaunawa.

Sakamakon sulhun na iya yin tasiri sosai ga harkokin kudi na Nijeriya da kuma makomar aikin wutar lantarki na Mambilla da aka dade ana jan kafa.

A halin yanzu dai Tsohon Shugaban Kasa Olusegun Obasanjo yana Birnin Paris don karrama goron gayyatar da aka yi masa na yin jawabi kan aikin samar da wutar lantarkin Mambila.

LEADERSHIP ta nakalto cewa tsohon shugaban ya bar Nijeriya zuwa Birnin Paris a safiyar ranar Asabar domin samun damar bayyana ya kuma yi magana a kan lamarin, wanda zai iya ci gaba da tafiya kamar yadda muke magana.

Mataimaki na musamman ga Obasanjo kan harkokin yada labarai, Kehinde Akin Yemi, ya tabbatar wa LEADERSHIP a ranar Litinin da yamma a Abeokuta cewa Obasanjo ya zabi girmama gayyatar ne domin daidaita al’amura.

Mambilla
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi
Manyan Labarai

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53
Manyan Labarai

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Next Post
Yadda Ficewar Kwararrun Ma’aikata Daga Nijeriya Ke Barazana Ga Tattalin Arzikin Kasa

Yadda Ficewar Kwararrun Ma’aikata Daga Nijeriya Ke Barazana Ga Tattalin Arzikin Kasa

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.