• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bai Dace Takara Ta Zamo Kalmar Kwatanta Alakar Sin Da Amurka Ba

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Bai Dace Takara Ta Zamo Kalmar Kwatanta Alakar Sin Da Amurka Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A shekarun baya bayan nan, mahukuntan kasar Amurka na yawaita jaddada kalmar Takara, a lokutan da suke tattauna batun alakar kasar su da Sin, har ma wannan kalma na neman zama tamkar ita ce Jigon” cudanyar sassan biyu.

Matakai daban daban da gwamnatin Amurka ke dauka, sun bayyana a fili yadda wannan kalma ta “Takara” ta shiga bakin kusoshin gwamnatin kasar, inda take wakiltar matakan nuna fin karfi, da kokarin dakile ci gaban Sin, da ma yiwa Sin din matsin lamba ta fannoni mabanbanta.

  • Shugaba Xi Jinping Da Takwaransa Na Afirka Ta Kudu Sun Jagoranci Taron Tattaunawa A Tsakanin Shugabannin Sin Da Afirka

To sai idan mun lura da matsayin kasashen biyu, abu ne mai kyau su yi takara mai tsafta a bangarori irin su cinikayya da raya fasahohi. Irin wadannan matakai na takara, ya dace su zamo bisa adalci, da kuma sanin ya kamata, kuma ya wajaba a gudanar da su kan tsari bisa dokoki tabbatattu.

Kaza lika, bai dace su zama matakai na watsi da dokokin raya tattalin arziki, da kuma sharuddan cudanyar sassan kasa da kasa ba. Har ila yau, bai dace a yi amfani da irin wadannan matakai wajen murgunawa wasu sassa ba.

Mun ga misalai da dama, dake nuna yadda Amurka karkashin manufar takara, take amfani da karfin ikonta wajen dakile ci gaban wasu kasashe, tare da salwantar da moriyar wasu kasashen, domin cimma nasarar takarar da ta sanya gaba. Hakika wannan dabara ta sabawa ainihin maanar takara mai kyau, maimakon haka, manufofi ne masu alaka da In ban samu ba, to kowa ya rasa da tunani irin na cacar baka.

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Sau da dama, mummunar takara daga bangaren Amurka na harzuka bangaren Sin, tare da lahanta moriyar kasar, da sukar manufofin ta musamman ta fuskar siyasa, da ikon mulkin kai, wanda hakan ya yi matukar keta hurumin kaidojin dangantakar kasa da kasa, da lahanta ginshikin cudanya a fannin siyasa tsakanin sassan biyu.

Don haka dai a takaice, maimakon ingiza matakan fito na fito, da rura wutar sabani da wariya, kamata ya yi sassan biyu su mayar da hankali ga bunkasa matakan cimma moriyar juna, da kyautata mutuntaka, da gudanar da takara a fannin inganta jagorancin alumma, da kiyaye moriyar ’yan kasa.

A matsayin Amurka da Sin na kasashe masu karfin tattalin arziki, kamata ya yi takararsu ta karkata ga nunawa duniya kyakkyawan misali, na yadda suke sauke nauyin bunkasa rayuwar alummunsu, da farfado da ci gaba bayan annoba, da shawo kan kalubalen sauyin yanayi, da matsalolin yankunansu, da kare kyakkyawan yanayin muhallin duniya, da wanzar da zaman lafiya, da samar da wadata ga alummun duniya kusan biliyan 8, ciki har da Sinawa da Amurkawa. (Saminu Alhassan)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Xi JinpingXinjiang
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yawan Jarin Da Sin Ta Zuba A Ketare Daga Janairu Zuwa Agusta Ya Rika Karuwa

Next Post

Sin Da Kasashe Masu Ra’ayi Iri Daya Sun Yi Kira Da A Inganta Rayuwar Mata Masu Bukata Ta Musamman A Cikin Al’umma

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

15 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

15 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

17 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

20 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

21 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

22 hours ago
Next Post
Sin Da Kasashe Masu Ra’ayi Iri Daya Sun Yi Kira Da A Inganta Rayuwar Mata Masu Bukata Ta Musamman A Cikin Al’umma

Sin Da Kasashe Masu Ra’ayi Iri Daya Sun Yi Kira Da A Inganta Rayuwar Mata Masu Bukata Ta Musamman A Cikin Al’umma

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.