• English
  • Business News
Monday, October 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bai Dace Takara Ta Zamo Kalmar Kwatanta Alakar Sin Da Amurka Ba

by CMG Hausa
2 years ago
Amurka

A shekarun baya bayan nan, mahukuntan kasar Amurka na yawaita jaddada kalmar Takara, a lokutan da suke tattauna batun alakar kasar su da Sin, har ma wannan kalma na neman zama tamkar ita ce Jigon” cudanyar sassan biyu.

Matakai daban daban da gwamnatin Amurka ke dauka, sun bayyana a fili yadda wannan kalma ta “Takara” ta shiga bakin kusoshin gwamnatin kasar, inda take wakiltar matakan nuna fin karfi, da kokarin dakile ci gaban Sin, da ma yiwa Sin din matsin lamba ta fannoni mabanbanta.

  • Shugaba Xi Jinping Da Takwaransa Na Afirka Ta Kudu Sun Jagoranci Taron Tattaunawa A Tsakanin Shugabannin Sin Da Afirka

To sai idan mun lura da matsayin kasashen biyu, abu ne mai kyau su yi takara mai tsafta a bangarori irin su cinikayya da raya fasahohi. Irin wadannan matakai na takara, ya dace su zamo bisa adalci, da kuma sanin ya kamata, kuma ya wajaba a gudanar da su kan tsari bisa dokoki tabbatattu.

Kaza lika, bai dace su zama matakai na watsi da dokokin raya tattalin arziki, da kuma sharuddan cudanyar sassan kasa da kasa ba. Har ila yau, bai dace a yi amfani da irin wadannan matakai wajen murgunawa wasu sassa ba.

Mun ga misalai da dama, dake nuna yadda Amurka karkashin manufar takara, take amfani da karfin ikonta wajen dakile ci gaban wasu kasashe, tare da salwantar da moriyar wasu kasashen, domin cimma nasarar takarar da ta sanya gaba. Hakika wannan dabara ta sabawa ainihin maanar takara mai kyau, maimakon haka, manufofi ne masu alaka da In ban samu ba, to kowa ya rasa da tunani irin na cacar baka.

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

Sau da dama, mummunar takara daga bangaren Amurka na harzuka bangaren Sin, tare da lahanta moriyar kasar, da sukar manufofin ta musamman ta fuskar siyasa, da ikon mulkin kai, wanda hakan ya yi matukar keta hurumin kaidojin dangantakar kasa da kasa, da lahanta ginshikin cudanya a fannin siyasa tsakanin sassan biyu.

Don haka dai a takaice, maimakon ingiza matakan fito na fito, da rura wutar sabani da wariya, kamata ya yi sassan biyu su mayar da hankali ga bunkasa matakan cimma moriyar juna, da kyautata mutuntaka, da gudanar da takara a fannin inganta jagorancin alumma, da kiyaye moriyar ’yan kasa.

A matsayin Amurka da Sin na kasashe masu karfin tattalin arziki, kamata ya yi takararsu ta karkata ga nunawa duniya kyakkyawan misali, na yadda suke sauke nauyin bunkasa rayuwar alummunsu, da farfado da ci gaba bayan annoba, da shawo kan kalubalen sauyin yanayi, da matsalolin yankunansu, da kare kyakkyawan yanayin muhallin duniya, da wanzar da zaman lafiya, da samar da wadata ga alummun duniya kusan biliyan 8, ciki har da Sinawa da Amurkawa. (Saminu Alhassan)

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

October 19, 2025
Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

October 19, 2025
Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka
Daga Birnin Sin

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

October 19, 2025
Next Post
Sin Da Kasashe Masu Ra’ayi Iri Daya Sun Yi Kira Da A Inganta Rayuwar Mata Masu Bukata Ta Musamman A Cikin Al’umma

Sin Da Kasashe Masu Ra’ayi Iri Daya Sun Yi Kira Da A Inganta Rayuwar Mata Masu Bukata Ta Musamman A Cikin Al’umma

LABARAI MASU NASABA

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

October 19, 2025
Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

October 19, 2025
Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

October 19, 2025
Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

October 19, 2025
Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

October 19, 2025
Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

October 19, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

October 19, 2025
Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

October 19, 2025
Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

October 19, 2025
Yadda Shagwaɓa Kananan Yara Da Kudi Ke Shafar Tarbiyyarsu

Yadda Shagwaɓa Kananan Yara Da Kudi Ke Shafar Tarbiyyarsu

October 19, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.