ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bai Kamata A Ba Emefiele Hutun Zuwa Karo Karatu Ba –Matawalle

by Sadiq
3 years ago
Matawalle

Gwamnan Jihar Zamfara, Bello Matawalle, ya kalubalanci matakin bai wa Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele dama ya tafi hutun karo karatu.

A cewar Matawalle, akwai bukatar Emefiele ya tsaya ya yi bayani game da “shirin samar da sabbin kudade mara kan-gado” da ya kirkiro, wanda ya jefa al’umar Nijeriya cikin mummunan yanayi.

  • Buhari Ya Yaba Wa Hilda Baci Kan Daukaka Nijeriya A Idon Duniya A Fannin Girke-Girke
  • Rikicin Sudan: Kashin Karshe Na ‘Yan Nijeriya Sun Iso Gida 

A makon da ya gabata rahotanni sun yi nuni da cewa Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya sahalewa Emefiele tafiya hutun karo karatu a kasar waje.

ADVERTISEMENT

Sai dai cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin, gwamna Matawalle, ya nemi Buhari da ya soke hutun domin Emefiele na da tarin batutuwan da ya kamata ya yi bayani a kai ga sabuwar gwamnatin Bola Ahmed Tinubu da ke shirin karbar mulki.

“Ina so na yi kira ga Shugaba Buhari, da kada ya amince da hutun zuwa karo karatu ga duk wani ma’aikaci da yake da muhimmiyar rawa da zai taka wajen ganin sabuwar gwamnatin Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ta fara aiki.

LABARAI MASU NASABA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

“Daya daga cikin wadannan mutane da rahotannin kafafen yada labarai ke cewa sun nemi izinin tafiya hutun karo karatu shi ne, Gwamnan Babban Bankin Nijeriya Godwin Emefiele.”

Gwamnan na Zamfara ya kara da cewa, Shugaba Buhari da mai dakinsa suna da kyakkyawar niyyar ganin an mika mulki salim-alim, “amma akwai wasu jami’ai da ke neman su haifar da rudani wajen tabbatar da aukuwar hakan.”

Matawalle sunan Emefiele kadai ya kama, bai ambaci sauran jami’an ba.

Jihar Zamfara na daya daga cikin jihohin da suka maka CBN a kotu wajen kalubalantar shirin sauya kudaden da aka yi.

Leadership Hausa ta ruwaito cewa fadar gwamnatin Nijeriya ta ce ba ta da masaniya kan shirin bai wa Emefiele hutun zuwa karo karatu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja
Manyan Labarai

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su
Manyan Labarai

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Next Post
Wani Mutum Ya Kashe Kishiyar Mahaifiyarsa A Kogi

Wani Mutum Ya Kashe Kishiyar Mahaifiyarsa A Kogi

LABARAI MASU NASABA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.