• Leadership Hausa
Tuesday, November 28, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bai Kamata A Ba Emefiele Hutun Zuwa Karo Karatu Ba –Matawalle

by Sadiq
7 months ago
in Manyan Labarai
0
Bai Kamata A Ba Emefiele Hutun Zuwa Karo Karatu Ba –Matawalle
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Bello Matawalle, ya kalubalanci matakin bai wa Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele dama ya tafi hutun karo karatu.

A cewar Matawalle, akwai bukatar Emefiele ya tsaya ya yi bayani game da “shirin samar da sabbin kudade mara kan-gado” da ya kirkiro, wanda ya jefa al’umar Nijeriya cikin mummunan yanayi.

  • Buhari Ya Yaba Wa Hilda Baci Kan Daukaka Nijeriya A Idon Duniya A Fannin Girke-Girke
  • Rikicin Sudan: Kashin Karshe Na ‘Yan Nijeriya Sun Iso Gida 

A makon da ya gabata rahotanni sun yi nuni da cewa Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya sahalewa Emefiele tafiya hutun karo karatu a kasar waje.

Sai dai cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin, gwamna Matawalle, ya nemi Buhari da ya soke hutun domin Emefiele na da tarin batutuwan da ya kamata ya yi bayani a kai ga sabuwar gwamnatin Bola Ahmed Tinubu da ke shirin karbar mulki.

“Ina so na yi kira ga Shugaba Buhari, da kada ya amince da hutun zuwa karo karatu ga duk wani ma’aikaci da yake da muhimmiyar rawa da zai taka wajen ganin sabuwar gwamnatin Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ta fara aiki.

Labarai Masu Nasaba

Kasurgumin Dan Daba, Hantar Daba Ya Mika Kansa Ga ‘Yansanda A Kano

‘Yansanda Sun Yi Barazanar Sa Kafar Wando Daya Da Masu Yunkurin Tada Hargitsi A Kano

“Daya daga cikin wadannan mutane da rahotannin kafafen yada labarai ke cewa sun nemi izinin tafiya hutun karo karatu shi ne, Gwamnan Babban Bankin Nijeriya Godwin Emefiele.”

Gwamnan na Zamfara ya kara da cewa, Shugaba Buhari da mai dakinsa suna da kyakkyawar niyyar ganin an mika mulki salim-alim, “amma akwai wasu jami’ai da ke neman su haifar da rudani wajen tabbatar da aukuwar hakan.”

Matawalle sunan Emefiele kadai ya kama, bai ambaci sauran jami’an ba.

Jihar Zamfara na daya daga cikin jihohin da suka maka CBN a kotu wajen kalubalantar shirin sauya kudaden da aka yi.

Leadership Hausa ta ruwaito cewa fadar gwamnatin Nijeriya ta ce ba ta da masaniya kan shirin bai wa Emefiele hutun zuwa karo karatu.

Tags: BuhariCBNEmefieleGwamnan ZamfaraHutun KaratuMatawalle
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kwanturolan NIS Reshen Ribas Ya Nemi Kara Inganta Kwazon Kwararrun ‘Yan Nijeriya

Next Post

Wani Mutum Ya Kashe Kishiyar Mahaifiyarsa A Kogi

Related

Kasurgumin Dan Daba, Hantar Daba Ya Mika Kansa Ga ‘Yansanda A Kano
Manyan Labarai

Kasurgumin Dan Daba, Hantar Daba Ya Mika Kansa Ga ‘Yansanda A Kano

2 hours ago
‘Yansanda Sun Yi Barazanar Sa Kafar Wando Daya Da Masu Yunkurin Tada Hargitsi A Kano
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Yi Barazanar Sa Kafar Wando Daya Da Masu Yunkurin Tada Hargitsi A Kano

8 hours ago
Kakakin Majalisar Kaduna
Manyan Labarai

Da Dumi-dumi: Kotun Daukaka Kara Ta Soke Zaben Kakakin Majalisar Kaduna

1 day ago
DA DUMI-DUMI: Gobara Ta Tashi A Babbar Kasuwar Kabba Ta Jihar Kogi
Manyan Labarai

DA DUMI-DUMI: Gobara Ta Tashi A Babbar Kasuwar Kabba Ta Jihar Kogi

1 day ago
Za Mu Samar Da Wutar Lantarki MW60 Ko Sola MW50 A Kowace Jiha -Gwamnonin Arewa Maso-Gabas
Manyan Labarai

Za Mu Samar Da Wutar Lantarki MW60 Ko Sola MW50 A Kowace Jiha -Gwamnonin Arewa Maso-Gabas

2 days ago
Sojoji Da ‘Yan banga Sun Ceto Mutum 6 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Kebbi
Manyan Labarai

Sojoji Da ‘Yan banga Sun Ceto Mutum 6 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Kebbi

2 days ago
Next Post
Wani Mutum Ya Kashe Kishiyar Mahaifiyarsa A Kogi

Wani Mutum Ya Kashe Kishiyar Mahaifiyarsa A Kogi

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Shugabanci: PTD Ta Ce Kwamared Egbon Kawai Ta Sani A Kaduna

Rikicin Shugabanci: PTD Ta Ce Kwamared Egbon Kawai Ta Sani A Kaduna

November 28, 2023
Li Qiang Ya Halarci Bikin CISCE Tare Da Gabatar Da Jawabi

Li Qiang Ya Halarci Bikin CISCE Tare Da Gabatar Da Jawabi

November 28, 2023
Xi Ya Jaddada Bukatar Raya Tsarin Shari’a Mai Nasaba Da Ketare

Xi Ya Jaddada Bukatar Raya Tsarin Shari’a Mai Nasaba Da Ketare

November 28, 2023
Kasurgumin Dan Daba, Hantar Daba Ya Mika Kansa Ga ‘Yansanda A Kano

Kasurgumin Dan Daba, Hantar Daba Ya Mika Kansa Ga ‘Yansanda A Kano

November 28, 2023
‘Yansanda Sun Kashe Shugabannin ‘Yan Ta’adda 3 A Jihar Katsina

‘Yansanda Sun Kashe Shugabannin ‘Yan Ta’adda 3 A Jihar Katsina

November 28, 2023
Fintiri Ya Sanar Da Tallafin Dubu 10 Ga ‘Yan Bautar Ƙasa A Adamawa

Fintiri Ya Sanar Da Tallafin Dubu 10 Ga ‘Yan Bautar Ƙasa A Adamawa

November 28, 2023
Gwamnati Ta Amince A Kashe Naira Biliyan N110 Don Gyare-gyaren Tituna A Fadin Nijeriya

Gwamnati Ta Amince A Kashe Naira Biliyan N110 Don Gyare-gyaren Tituna A Fadin Nijeriya

November 28, 2023
Kakakin Majalisar Bauchi

Kotun Daukaka Kara Ta Soke Zaben Mataimakin Kakakin Majalisar Bauchi

November 28, 2023
UEFA Champions League: Za Mu Taka Leda Tamkar  A Wasan Karshe – Xavi

UEFA Champions League: Za Mu Taka Leda Tamkar  A Wasan Karshe – Xavi

November 28, 2023
‘Yansanda Sun Yi Barazanar Sa Kafar Wando Daya Da Masu Yunkurin Tada Hargitsi A Kano

‘Yansanda Sun Yi Barazanar Sa Kafar Wando Daya Da Masu Yunkurin Tada Hargitsi A Kano

November 28, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.