• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bai Kamata Gwamnatin Tinubu Ta Bi Sahun Ta Buhari Ba —Shugaban EYN

by Muh'd Shafi'u Saleh
2 years ago
in Labarai
0
Bai Kamata Gwamnatin Tinubu Ta Bi Sahun Ta Buhari Ba —Shugaban EYN
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An nuna damuwa game da basussukan da gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari, ta ciyo, rashin aikin yi ga matasa, da cewa bai kamata sabuwar gwamnati mai zuwa ta bi sahunta ba.

Shugaban mujami’ar majalisar ‘yan uwa a Nijeriya (EYN), Rabaran Joel Billi, ya bayyana haka a taron fastoci da wakilan mujami’ar karo na 76, da ya gudana a hedikwatar cocin da ke Kwarhi a karamar hukumar Hong a jihar Adamawa.

  • Mukaddashin Mataimakin Shugaban Jami’ar Modibbo Adama Ya Rasu
  • NNPP Ba Ta Da Kudin Kalubalantar Nasarar Tinubu A Kotu –Buba Galadima

Ya ci gaba da cewa “Wannan bashin ba zai kyale sabuwar gwamnati mai zuwa ta iya samar da abubuwan more rayuwa ga al’ummar kasar nan ko aikin yi ga matasa ba.

“Da kamar wuya gwamnati mai zuwa ta iya biyan basusukan da ake bin Nijeriya kuma ta samu zarafin gudanar da ayyukan ci gaban kasa.

“Ina kira ga gwamnati mai shigowa da ta zama mai sauraren jama’a, ta rika bibiya da jin koke-koken mutane, ba kamar yadda gwamnatin shugaba Buhari ta yi kememe kan batun El-Zakzaky,” ya jaddada.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

Da yake magana game da taron fastocin cocin da ya gudana a ranar Alhamis, shugaban cocin ya ce “taronmu ya cimma nasarori, muna fatan fastoci da wakilai, za su yi amfani da irin koyarwar da su ka samu, hadi kan al’ummar Nijeriya shi zai tabbatar da kasarmu ta zauna lafiya a matsayin abu daya” in ji Billi.

A karin bayanin da ya yi wa manema labarai, babban sakataren gudanarwar mujami’ar na kasa, Rabaran Dakta Daniel Mbaya, ya ce taron ke da alhakin zartar da kodurorin da cocin za ta aiwatar a shekarar nan da ma shekara mai zuwa.

Ya ce mahalarta taron sun fito ne daga jihohin kasar nan, da wasu kasashen duniya, inda ya ce manufar taron shi ne samar da ingantaccen zaman lafiya tsakanin Musulmi da Kirista da ma wadanda ba su da kowane Addini.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BashiBuhariFastogwamnatiTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tattalin Arzikin Kasar Sin Yana Kan Tubali Mai Kwari

Next Post

Shugaban Sashen Fassara Na Leadership Hausa, Malam Sabo Ahmad Ya Rasu

Related

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo
Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

9 minutes ago
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas
Labarai

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

4 hours ago
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa
Manyan Labarai

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

5 hours ago
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano
Labarai

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

7 hours ago
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark
Labarai

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

8 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara
Labarai

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

11 hours ago
Next Post
Shugaban Sashen Fassara Na Leadership Hausa, Malam Sabo Ahmad Ya Rasu

Shugaban Sashen Fassara Na Leadership Hausa, Malam Sabo Ahmad Ya Rasu

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

July 27, 2025
Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

July 27, 2025
Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

July 27, 2025
Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

July 27, 2025
Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

July 27, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

July 27, 2025
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

July 27, 2025
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.