• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bai Kamata Gwamnatin Tinubu Ta Bi Sahun Ta Buhari Ba —Shugaban EYN

by Muh'd Shafi'u Saleh
2 years ago
in Labarai
0
Bai Kamata Gwamnatin Tinubu Ta Bi Sahun Ta Buhari Ba —Shugaban EYN
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An nuna damuwa game da basussukan da gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari, ta ciyo, rashin aikin yi ga matasa, da cewa bai kamata sabuwar gwamnati mai zuwa ta bi sahunta ba.

Shugaban mujami’ar majalisar ‘yan uwa a Nijeriya (EYN), Rabaran Joel Billi, ya bayyana haka a taron fastoci da wakilan mujami’ar karo na 76, da ya gudana a hedikwatar cocin da ke Kwarhi a karamar hukumar Hong a jihar Adamawa.

  • Mukaddashin Mataimakin Shugaban Jami’ar Modibbo Adama Ya Rasu
  • NNPP Ba Ta Da Kudin Kalubalantar Nasarar Tinubu A Kotu –Buba Galadima

Ya ci gaba da cewa “Wannan bashin ba zai kyale sabuwar gwamnati mai zuwa ta iya samar da abubuwan more rayuwa ga al’ummar kasar nan ko aikin yi ga matasa ba.

“Da kamar wuya gwamnati mai zuwa ta iya biyan basusukan da ake bin Nijeriya kuma ta samu zarafin gudanar da ayyukan ci gaban kasa.

“Ina kira ga gwamnati mai shigowa da ta zama mai sauraren jama’a, ta rika bibiya da jin koke-koken mutane, ba kamar yadda gwamnatin shugaba Buhari ta yi kememe kan batun El-Zakzaky,” ya jaddada.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

Da yake magana game da taron fastocin cocin da ya gudana a ranar Alhamis, shugaban cocin ya ce “taronmu ya cimma nasarori, muna fatan fastoci da wakilai, za su yi amfani da irin koyarwar da su ka samu, hadi kan al’ummar Nijeriya shi zai tabbatar da kasarmu ta zauna lafiya a matsayin abu daya” in ji Billi.

A karin bayanin da ya yi wa manema labarai, babban sakataren gudanarwar mujami’ar na kasa, Rabaran Dakta Daniel Mbaya, ya ce taron ke da alhakin zartar da kodurorin da cocin za ta aiwatar a shekarar nan da ma shekara mai zuwa.

Ya ce mahalarta taron sun fito ne daga jihohin kasar nan, da wasu kasashen duniya, inda ya ce manufar taron shi ne samar da ingantaccen zaman lafiya tsakanin Musulmi da Kirista da ma wadanda ba su da kowane Addini.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BashiBuhariFastogwamnatiTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tattalin Arzikin Kasar Sin Yana Kan Tubali Mai Kwari

Next Post

Shugaban Sashen Fassara Na Leadership Hausa, Malam Sabo Ahmad Ya Rasu

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

9 minutes ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

3 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

4 hours ago
Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

13 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

15 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

16 hours ago
Next Post
Shugaban Sashen Fassara Na Leadership Hausa, Malam Sabo Ahmad Ya Rasu

Shugaban Sashen Fassara Na Leadership Hausa, Malam Sabo Ahmad Ya Rasu

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.