ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NNPP Ba Ta Da Kudin Kalubalantar Nasarar Tinubu A Kotu –Buba Galadima

by Abubakar Abba
3 years ago
NNPP

Jigo a jam’iyyar NNPP Buba Galadima ya bayyana cewa, NNPP taki kalubalantar nasarar da zababben shugaban kasa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya samu a zaben shugaban kasa na 2023 a gaban kotu ne, domin ba ta da kudin da za ta yi hakan.

Galadima ya sanar da hakan ne a hirarsa da gidan talabijin na ARISE a kan ganawar sirri da tsakanin Sanata Rabiu Musa Kwankwaso na NNPP da Tinubu a kasar Faransa.

  • EFCC Na Binciken Gwamnan Zamfara Kan Almundahanar Biliyan 70
  • Xi Da Mai Dakinsa Sun Jagoranci Bikin Maraba Da Baki Mahalarta Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

An ruwaito cewa, Tinubu ya yi ganawar sirrin ne da Kwakwaso don ya samar da masahala a tsakanin Kwankwaso da Abdulmumin Jibrin, tsohon jami’in yakin neman zaben Tinubu kuma zababben dan majalisar wakilai da ya sauya sheka zuwa NNPP daga APC kafin zaben 2023.

ADVERTISEMENT

Sai dai, ba a samun cikakkun bayanai kan ganawar sirrin da Tinubu ya yi da Kwankwaso ba, amma an ce, sun tattauna kan kafa gwamnatin hadin kan kasa a tsakanin jami’iyyun biyu.

Galadima da yake mayar da martani kan ganawar sirrin ta manayn ‘yan siyasar biyu ya ce, babu wani labari domin abu ne da bisa tahirin siyasar Nijeriya, hakan ya saba farauwa.

LABARAI MASU NASABA

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ya ci gaba da cewa, komai yau a Nijeriya ya na zama labarai, inda ya ce, ganawar a tsakanin jagororin ‘yan siyasar biyu, bai kamata ace ta ja hankalin mutane ba.

Ya ci gaba da cewa, kamar yadda ku ka sani ne, Kwankwaso ya yi takarar shugaban kasa da Tinubu a 2023, inda NNPP ta zo na hudu, inda ya sanar da cewa, NNPP ce kawai ba ta je kotu ba, wanda mune ke da cikakkun dalilan zuwa kotu.

A cewarsa, ganawar sirri irin wannan da kuma tunanin kafa gwmnatin hada kan kasa, ba sabon abu ne a harkar siyasar Nijeriya ba domin irin wannan, ta taba faruwa a jamhuriya ta farko a tsakanin jami’yyun NCNC da NPC a taakanin jam’iyyun Azikiwe da Ahmadu Bello.

Ya bayyana cewa, daga baya sun kafa gwmnatin hada kan kasa a tsakanin NPC da NNDP wadda Cif Samuel Akintola na gabas ya jagoranta.

Ya kara da cewa, har ila yau, a rubuce yake a lokacin gwamnatin Shagari, jami’yyar NPP da Nnamdi Azikiwe ke jagoranta, sun kulla yarjejeniya da gwmnatin NPN.

Galadima ya yi nuni da cewa, wannan tarihi ne ya sake mai-maita kansa, a saboda haka ya na da kyau a ilimantar da matasa kan tarihin kasar su.

Da yake mayar da martani kan abinda yasa NNPP ba ta kalubalanci nasarar Tinubu a kotu kamar yadda PDP da LP da sauran jami’iyyu suka yi, ba Galadima ya ce, NNPP ba ta da wadatattun kudin da za ta yi hakan.

Ya ce, wannan abun a rubuce yake cewa, PDP ce ta kore mu ni da Kwankwaso, ba wai mun shiga takarar don mu dakatar da su daga cin nasara a zaben bane.

Ya ce, muna sane da cewa, zuwa kotu na bukatar kudade masu yawa wanda bamu da su, inda ya ce, duk wanda zai je kotu don kalubalantar zabe, akalla sai ya tanadi Naira biliyan biyar, mu kuma, ba mu da wadannan kudaden.

NNPP
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI
Ra'ayi Riga

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya
Labarai

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
Next Post
Matsalar Kasa Biyan Basusukan Da Amurka Take Fuskanta Za Ta Kawowa Duniya Asara

Matsalar Kasa Biyan Basusukan Da Amurka Take Fuskanta Za Ta Kawowa Duniya Asara

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.