• English
  • Business News
Thursday, July 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NNPP Ba Ta Da Kudin Kalubalantar Nasarar Tinubu A Kotu –Buba Galadima

by Abubakar Abba
2 years ago
in Labarai
0
NNPP Ba Ta Da Kudin Kalubalantar Nasarar Tinubu A Kotu –Buba Galadima
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jigo a jam’iyyar NNPP Buba Galadima ya bayyana cewa, NNPP taki kalubalantar nasarar da zababben shugaban kasa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya samu a zaben shugaban kasa na 2023 a gaban kotu ne, domin ba ta da kudin da za ta yi hakan.

Galadima ya sanar da hakan ne a hirarsa da gidan talabijin na ARISE a kan ganawar sirri da tsakanin Sanata Rabiu Musa Kwankwaso na NNPP da Tinubu a kasar Faransa.

  • EFCC Na Binciken Gwamnan Zamfara Kan Almundahanar Biliyan 70
  • Xi Da Mai Dakinsa Sun Jagoranci Bikin Maraba Da Baki Mahalarta Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

An ruwaito cewa, Tinubu ya yi ganawar sirrin ne da Kwakwaso don ya samar da masahala a tsakanin Kwankwaso da Abdulmumin Jibrin, tsohon jami’in yakin neman zaben Tinubu kuma zababben dan majalisar wakilai da ya sauya sheka zuwa NNPP daga APC kafin zaben 2023.

Sai dai, ba a samun cikakkun bayanai kan ganawar sirrin da Tinubu ya yi da Kwankwaso ba, amma an ce, sun tattauna kan kafa gwamnatin hadin kan kasa a tsakanin jami’iyyun biyu.

Galadima da yake mayar da martani kan ganawar sirrin ta manayn ‘yan siyasar biyu ya ce, babu wani labari domin abu ne da bisa tahirin siyasar Nijeriya, hakan ya saba farauwa.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

Ya ci gaba da cewa, komai yau a Nijeriya ya na zama labarai, inda ya ce, ganawar a tsakanin jagororin ‘yan siyasar biyu, bai kamata ace ta ja hankalin mutane ba.

Ya ci gaba da cewa, kamar yadda ku ka sani ne, Kwankwaso ya yi takarar shugaban kasa da Tinubu a 2023, inda NNPP ta zo na hudu, inda ya sanar da cewa, NNPP ce kawai ba ta je kotu ba, wanda mune ke da cikakkun dalilan zuwa kotu.

A cewarsa, ganawar sirri irin wannan da kuma tunanin kafa gwmnatin hada kan kasa, ba sabon abu ne a harkar siyasar Nijeriya ba domin irin wannan, ta taba faruwa a jamhuriya ta farko a tsakanin jami’yyun NCNC da NPC a taakanin jam’iyyun Azikiwe da Ahmadu Bello.

Ya bayyana cewa, daga baya sun kafa gwmnatin hada kan kasa a tsakanin NPC da NNDP wadda Cif Samuel Akintola na gabas ya jagoranta.

Ya kara da cewa, har ila yau, a rubuce yake a lokacin gwamnatin Shagari, jami’yyar NPP da Nnamdi Azikiwe ke jagoranta, sun kulla yarjejeniya da gwmnatin NPN.

Galadima ya yi nuni da cewa, wannan tarihi ne ya sake mai-maita kansa, a saboda haka ya na da kyau a ilimantar da matasa kan tarihin kasar su.

Da yake mayar da martani kan abinda yasa NNPP ba ta kalubalanci nasarar Tinubu a kotu kamar yadda PDP da LP da sauran jami’iyyu suka yi, ba Galadima ya ce, NNPP ba ta da wadatattun kudin da za ta yi hakan.

Ya ce, wannan abun a rubuce yake cewa, PDP ce ta kore mu ni da Kwankwaso, ba wai mun shiga takarar don mu dakatar da su daga cin nasara a zaben bane.

Ya ce, muna sane da cewa, zuwa kotu na bukatar kudade masu yawa wanda bamu da su, inda ya ce, duk wanda zai je kotu don kalubalantar zabe, akalla sai ya tanadi Naira biliyan biyar, mu kuma, ba mu da wadannan kudaden.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCBuba GaladimaKwankwasoNNPPTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

EFCC Na Binciken Gwamnan Zamfara Kan Almundahanar Biliyan 70

Next Post

Matsalar Kasa Biyan Basusukan Da Amurka Take Fuskanta Za Ta Kawowa Duniya Asara

Related

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas
Labarai

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

7 hours ago
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano
Labarai

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

9 hours ago
Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC
Labarai

Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

10 hours ago
Kayan Aro Baya Rufe Katara
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa JKS Mai Tsawon Tarihin Sama Da Shekaru 100 Ta Dore A Kan Mulki

12 hours ago
Atiku, Obi, El-Rufai, Amaechi Da Wasu Sun Halarci Taron ADC Na jam’iyyar Haɗaka
Manyan Labarai

Atiku, Obi, El-Rufai, Amaechi Da Wasu Sun Halarci Taron ADC Na jam’iyyar Haɗaka

12 hours ago
Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump
Kasashen Ketare

Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump

15 hours ago
Next Post
Matsalar Kasa Biyan Basusukan Da Amurka Take Fuskanta Za Ta Kawowa Duniya Asara

Matsalar Kasa Biyan Basusukan Da Amurka Take Fuskanta Za Ta Kawowa Duniya Asara

LABARAI MASU NASABA

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

July 2, 2025
Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

July 2, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

July 2, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

July 2, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

July 2, 2025
Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma

Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma

July 2, 2025
Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

July 2, 2025
Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5

Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5

July 2, 2025
Rukunin Ƴan APC A Kano Sun Nemi A Rushe Jagorancin Jam’iyyar A Jihar

Rukunin Ƴan APC A Kano Sun Nemi A Rushe Jagorancin Jam’iyyar A Jihar

July 2, 2025
Xi Ya Bukaci Kungiyoyin Matasa Da Dalibai Su Zurfafa Gyare-Gyare Da Kirkire-Kirkire Don Samun Sabbin Nasarori

Xi Ya Bukaci Kungiyoyin Matasa Da Dalibai Su Zurfafa Gyare-Gyare Da Kirkire-Kirkire Don Samun Sabbin Nasarori

July 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.