• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bajintar Aiki: Majalisar Dattawa Ta Jinjina Wa Ministan Yaɗa Labarai

...Ta Nemi Karin Kasafin Kuɗi Ga Ma’aikatar yada labarai da wayar da kai

by Sulaiman
8 months ago
in Labarai
0
Bajintar Aiki: Majalisar Dattawa Ta Jinjina Wa Ministan Yaɗa Labarai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar Dattawa ta yaba wa Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, bisa ƙoƙarinsa wajen gudanarwa da yaɗa bayanai kan manufofi da shirye-shiryen gwamnati.  

 

An yi masa wannan yabon ne a ranar Talata yayin da ya bayyana a gaban Kwamitin Majalisar Dattawa kan Yaɗa Labarai don kare kasafin kuɗin ma’aikatarsa na shekarar 2025.

  • Arsenal Ta Matsawa Liverpool Ƙaimi Bayan Doke Tottenham A Emirates 
  • Karkashin BRI Sin Ta Yi Hadin Gwiwar Samar Da Dakunan Gwaje-gwaje Sama Da 70

Sanatocin sun jinjina wa ƙoƙarin ma’aikatar amma sun nuna damuwa kan ƙarancin kuɗaɗen da aka ware mata, suna masu cewa ba zai wadatar ba don aiwatar da aikin ta na yaɗa labarai kan manufofi da shirye-shiryen gwamnati.

 

Labarai Masu Nasaba

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

Sun buƙaci a samar da ƙarin kasafin kuɗi na musamman domin a ƙarfafa wa ma’aikatar gwiwa.

 

Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan (PDP-Kogi) ta jaddada bambancin kasafin kuɗin ma’aikatar da na ƙasar Afirka ta Kudu, inda ta bayyana cewa Ma’aikatar Yaɗa Labarai ta Afirka ta Kudu ta samu kimanin naira biliyan 409 don aiwatar da shirye-shiryen ta.

 

Ta ce Nijeriya, wadda ke da yawan al’umma fiye da waccan ƙasar, ya kamata ta ware ƙarin kuɗi don shirye-shiryen ta na yaɗa labarai.

 

Ta kuma jaddada muhimmancin wayar da kan al’umma, musamman matasa, da kuma yadda ministan da tawagar sa suke shirye don aiwatar da hakan idan aka ƙara masu kuɗi.

 

Shi kuwa Sanata Abdul Ningi (PDP-Bauchi) ya yaba wa ministan bisa ƙwarewar sa, jagorancin sa, da kuma cigaban da aka samu a hukumomin da ke ƙarƙashin ma’aikatar, musamman ta fuskar cigaba da aka samu a Hukumar Tlabijin ta Nijeriya (NTA).

 

A nasa jawabin, Shugaban Kwamitin, Sanata Ken Eze (APC-Ebonyi), ya buƙaci ma’aikatar da ta ƙirƙiro hanyoyin samun kuɗaɗen shiga.

 

Ya kuma buƙaci a sake duba kasafin kuɗin, yana mai jaddada muhimmancin ɓangaren yaɗa labarai ga nasarar gwamnati.

 

Ya ce: “Ba za a iya yin abubuwa da yawa ba idan babu kuɗaɗen shiga, kuma bayanai suna da matuƙar muhimmanci: muna buƙatar ɓangaren ya jagoranci manufofi da shirye-shiryen gwamnati.

 

“Kasafin kuɗin da ke gaban mu ba abin alfahari ba ne, idan an yi la’akari da abin da ake yi a wasu ƙasashe.

 

“Dole ne mu yi magana a matsayin ‘yan majalisa; dole ne mu ƙi amincewa da kasafin kuɗin ta hanyar kiran a ƙara yawan kasafin da aka ware wa ma’aikatar.

 

“Muna so Ministan Kasafi da Tsare-tsare na Ƙasa ya bayyana a gaban mu don sake duba kasafin kuɗin.”

 

A baya, ministan ya ƙiyasta cewa mafi ƙarancin adadin da ake buƙata don gudanar da ayyukan ma’aikatar yadda ya kamata ya kai naira biliyan 50.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu Ta Ɗaure Wasu Mutane 4 Da Ake Zargi Da Satar Birkin Jirgin Sama Guda 80 A Kano

Next Post

Hisbah Ta Yi Kakkausan Gargaɗi Tare Da Kira Ga Iyaye Kan Kula Da Yara Bayan Samun Gawar Wasu 4

Related

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

53 minutes ago
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
Da ɗumi-ɗuminsa

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

3 hours ago
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
Labarai

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

4 hours ago
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

6 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja
Labarai

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

7 hours ago
Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu
Labarai

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

8 hours ago
Next Post
Hisbah Ta Yi Kakkausan Gargaɗi Tare Da Kira Ga Iyaye Kan Kula Da Yara Bayan Samun Gawar Wasu 4

Hisbah Ta Yi Kakkausan Gargaɗi Tare Da Kira Ga Iyaye Kan Kula Da Yara Bayan Samun Gawar Wasu 4

LABARAI MASU NASABA

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

September 17, 2025
Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

September 17, 2025
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

September 17, 2025
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

September 17, 2025
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

September 17, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

September 17, 2025
Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

September 17, 2025
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

September 17, 2025
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.