• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ban Taba Ba Ministan Shari’a Da CBN Umarnin Su Ki Mutunta Hukuncin Kotun Koli Ba – Buhari

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Buhari

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari, ya yi martani kan wasu batutuwa da wasu mutane ke cewa shi din ya ki cewa uffan kan umarnin da babban kotun koli ta bayar na sake fitar da takardar tsoffin kudi na N500 da N1,000, ya ce, shi babu wani lokaci da ya umarci ministan Shari’a kuma Antoni Janar na kasa (AGF) ko gwamnan babban bankin Nijeriya (CBN) da su ki ko su yi kunnen uwar shegu da umarnin Kotun.

 

Shugaban ya ce, baya daga cikin dabi’arsa kwata-kwata da ya umarci hadimansa wajen kin mutunta hukuncin kotuna kan lamuran da suka shafi gwamnati da wasu bangarori.

  • Buhari Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Gwarzon Dan Siyasa, Musa Musawa

A cewar wata sanarwar da Kakakin shugaban, Malam Garba Shehu da ya fitar a ranar Litinin, ya ce, Buharin tun lokacin da ya shiga ofis a shekarar 2015, bai taba umartar wani mutum da ya yi bore wa umarnin kotuna ba, ya yi imanin cewa demurudiyya ba za ta samu yadda ake bukata ba muddin babu doka.

 

LABARAI MASU NASABA

Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

“Kan halin da ake ciki na batun tsoffin kudade, akwai bukatar jama’a su sani shugaba Buhari bai yi komai wajen kawo cikas ga sashin shari’a ba.

 

“Bai taka burkin ko hana Antoni Janar da gwamnan CBN daga gudanar da ayyukansu da doka ya tadanar ba. Don haka babu wata shaida da za ta iya nuna cewa shi din ya hana mutanen biyu biyaya ga umarnin babban kotun.

 

“Shi dai shugaban kasa bayan ganawar da ya yi da Majalisar Kolin kasa. Ya umarci banki da ya tabbatar ya wadatar al’ummar kasa da takardun kudade da suke bukata, kuma babu wani abun da ya canza wannan matsayin nasa.

 

“Wannan kadai ya ishi al’umma su fahimci cewa shugaba Buhari na matukar mutunta umarnin kotuna.”

 

Sanarwar ta ce, hatta kesa-kesan da suka shafi cin hanci da rashawa, shugaban baya katsalandan wa harkar shari’a balle ma ya tsoma bakinsa domin yana barin kotuna su yi aikinsu yadda doka ya tanadar.

 

Garba Shehu ya ce, masu tashi haikan wajen ganin sun bata sunan Buhari da shafa masa kashin kaji na rashin biyayya ga kotu kai tsaye hakan rashin adalci muraran, “Domin babu wani umarnin kotu a kowace gaba da aka yi kai tsaye ga shi ‘Buhari’ a kashin kansa.”

 

“CBN bai da wani dalilin da zai ki biyayya wa umarnin kotu ya ce yana zaman jiran umarnin shugaban kasa,” Garba ya kara.

 

Buhari ya kuma karyata jita-jitan da wasu ke yi na cewa gwamamtinsa ta kawo tsare-tsaren da suka ruguza sashin tattalin arziki, yana mai cewa Babu wata gwamnatin da ta fito da tsare-tsare da kyawawan manufofin bunkasa tattalin arziki irin tasa gwamnatin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos
Labarai

Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

November 6, 2025
Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata
Labarai

Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

November 6, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Majalisa Ta Ɗage Tantance Ministan Tinubu Saboda Rashin Rahoton Tsaro

November 6, 2025
Next Post
Noma

Da Dumi-Dumi: CBN Ya Amince Da Ci Gaba Da Amfani Da Tsofaffin Takardun Naira

LABARAI MASU NASABA

Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

November 6, 2025
Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

November 6, 2025
Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

November 6, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Majalisa Ta Ɗage Tantance Ministan Tinubu Saboda Rashin Rahoton Tsaro

November 6, 2025
Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Majalisar Dattawa

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.