• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ban Taba Ba Ministan Shari’a Da CBN Umarnin Su Ki Mutunta Hukuncin Kotun Koli Ba – Buhari

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Buhari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari, ya yi martani kan wasu batutuwa da wasu mutane ke cewa shi din ya ki cewa uffan kan umarnin da babban kotun koli ta bayar na sake fitar da takardar tsoffin kudi na N500 da N1,000, ya ce, shi babu wani lokaci da ya umarci ministan Shari’a kuma Antoni Janar na kasa (AGF) ko gwamnan babban bankin Nijeriya (CBN) da su ki ko su yi kunnen uwar shegu da umarnin Kotun.

 

Shugaban ya ce, baya daga cikin dabi’arsa kwata-kwata da ya umarci hadimansa wajen kin mutunta hukuncin kotuna kan lamuran da suka shafi gwamnati da wasu bangarori.

  • Buhari Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Gwarzon Dan Siyasa, Musa Musawa

A cewar wata sanarwar da Kakakin shugaban, Malam Garba Shehu da ya fitar a ranar Litinin, ya ce, Buharin tun lokacin da ya shiga ofis a shekarar 2015, bai taba umartar wani mutum da ya yi bore wa umarnin kotuna ba, ya yi imanin cewa demurudiyya ba za ta samu yadda ake bukata ba muddin babu doka.

 

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

“Kan halin da ake ciki na batun tsoffin kudade, akwai bukatar jama’a su sani shugaba Buhari bai yi komai wajen kawo cikas ga sashin shari’a ba.

 

“Bai taka burkin ko hana Antoni Janar da gwamnan CBN daga gudanar da ayyukansu da doka ya tadanar ba. Don haka babu wata shaida da za ta iya nuna cewa shi din ya hana mutanen biyu biyaya ga umarnin babban kotun.

 

“Shi dai shugaban kasa bayan ganawar da ya yi da Majalisar Kolin kasa. Ya umarci banki da ya tabbatar ya wadatar al’ummar kasa da takardun kudade da suke bukata, kuma babu wani abun da ya canza wannan matsayin nasa.

 

“Wannan kadai ya ishi al’umma su fahimci cewa shugaba Buhari na matukar mutunta umarnin kotuna.”

 

Sanarwar ta ce, hatta kesa-kesan da suka shafi cin hanci da rashawa, shugaban baya katsalandan wa harkar shari’a balle ma ya tsoma bakinsa domin yana barin kotuna su yi aikinsu yadda doka ya tanadar.

 

Garba Shehu ya ce, masu tashi haikan wajen ganin sun bata sunan Buhari da shafa masa kashin kaji na rashin biyayya ga kotu kai tsaye hakan rashin adalci muraran, “Domin babu wani umarnin kotu a kowace gaba da aka yi kai tsaye ga shi ‘Buhari’ a kashin kansa.”

 

“CBN bai da wani dalilin da zai ki biyayya wa umarnin kotu ya ce yana zaman jiran umarnin shugaban kasa,” Garba ya kara.

 

Buhari ya kuma karyata jita-jitan da wasu ke yi na cewa gwamamtinsa ta kawo tsare-tsaren da suka ruguza sashin tattalin arziki, yana mai cewa Babu wata gwamnatin da ta fito da tsare-tsare da kyawawan manufofin bunkasa tattalin arziki irin tasa gwamnatin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Za Ta Taka Rawa A Harkokin Duniya Kamar Haka

Next Post

Da Dumi-Dumi: CBN Ya Amince Da Ci Gaba Da Amfani Da Tsofaffin Takardun Naira

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

55 minutes ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

4 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

4 hours ago
Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

14 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

16 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

17 hours ago
Next Post
Noma

Da Dumi-Dumi: CBN Ya Amince Da Ci Gaba Da Amfani Da Tsofaffin Takardun Naira

LABARAI MASU NASABA

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.