ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ban Taba Ba Ministan Shari’a Da CBN Umarnin Su Ki Mutunta Hukuncin Kotun Koli Ba – Buhari

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Buhari

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari, ya yi martani kan wasu batutuwa da wasu mutane ke cewa shi din ya ki cewa uffan kan umarnin da babban kotun koli ta bayar na sake fitar da takardar tsoffin kudi na N500 da N1,000, ya ce, shi babu wani lokaci da ya umarci ministan Shari’a kuma Antoni Janar na kasa (AGF) ko gwamnan babban bankin Nijeriya (CBN) da su ki ko su yi kunnen uwar shegu da umarnin Kotun.

 

Shugaban ya ce, baya daga cikin dabi’arsa kwata-kwata da ya umarci hadimansa wajen kin mutunta hukuncin kotuna kan lamuran da suka shafi gwamnati da wasu bangarori.

ADVERTISEMENT
  • Buhari Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Gwarzon Dan Siyasa, Musa Musawa

A cewar wata sanarwar da Kakakin shugaban, Malam Garba Shehu da ya fitar a ranar Litinin, ya ce, Buharin tun lokacin da ya shiga ofis a shekarar 2015, bai taba umartar wani mutum da ya yi bore wa umarnin kotuna ba, ya yi imanin cewa demurudiyya ba za ta samu yadda ake bukata ba muddin babu doka.

 

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

“Kan halin da ake ciki na batun tsoffin kudade, akwai bukatar jama’a su sani shugaba Buhari bai yi komai wajen kawo cikas ga sashin shari’a ba.

 

“Bai taka burkin ko hana Antoni Janar da gwamnan CBN daga gudanar da ayyukansu da doka ya tadanar ba. Don haka babu wata shaida da za ta iya nuna cewa shi din ya hana mutanen biyu biyaya ga umarnin babban kotun.

 

“Shi dai shugaban kasa bayan ganawar da ya yi da Majalisar Kolin kasa. Ya umarci banki da ya tabbatar ya wadatar al’ummar kasa da takardun kudade da suke bukata, kuma babu wani abun da ya canza wannan matsayin nasa.

 

“Wannan kadai ya ishi al’umma su fahimci cewa shugaba Buhari na matukar mutunta umarnin kotuna.”

 

Sanarwar ta ce, hatta kesa-kesan da suka shafi cin hanci da rashawa, shugaban baya katsalandan wa harkar shari’a balle ma ya tsoma bakinsa domin yana barin kotuna su yi aikinsu yadda doka ya tanadar.

 

Garba Shehu ya ce, masu tashi haikan wajen ganin sun bata sunan Buhari da shafa masa kashin kaji na rashin biyayya ga kotu kai tsaye hakan rashin adalci muraran, “Domin babu wani umarnin kotu a kowace gaba da aka yi kai tsaye ga shi ‘Buhari’ a kashin kansa.”

 

“CBN bai da wani dalilin da zai ki biyayya wa umarnin kotu ya ce yana zaman jiran umarnin shugaban kasa,” Garba ya kara.

 

Buhari ya kuma karyata jita-jitan da wasu ke yi na cewa gwamamtinsa ta kawo tsare-tsaren da suka ruguza sashin tattalin arziki, yana mai cewa Babu wata gwamnatin da ta fito da tsare-tsare da kyawawan manufofin bunkasa tattalin arziki irin tasa gwamnatin.

Buhari
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Next Post
Noma

Da Dumi-Dumi: CBN Ya Amince Da Ci Gaba Da Amfani Da Tsofaffin Takardun Naira

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.