ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ban Taba Ba Ministan Shari’a Da CBN Umarnin Su Ki Mutunta Hukuncin Kotun Koli Ba – Buhari

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Buhari

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari, ya yi martani kan wasu batutuwa da wasu mutane ke cewa shi din ya ki cewa uffan kan umarnin da babban kotun koli ta bayar na sake fitar da takardar tsoffin kudi na N500 da N1,000, ya ce, shi babu wani lokaci da ya umarci ministan Shari’a kuma Antoni Janar na kasa (AGF) ko gwamnan babban bankin Nijeriya (CBN) da su ki ko su yi kunnen uwar shegu da umarnin Kotun.

 

Shugaban ya ce, baya daga cikin dabi’arsa kwata-kwata da ya umarci hadimansa wajen kin mutunta hukuncin kotuna kan lamuran da suka shafi gwamnati da wasu bangarori.

ADVERTISEMENT
  • Buhari Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Gwarzon Dan Siyasa, Musa Musawa

A cewar wata sanarwar da Kakakin shugaban, Malam Garba Shehu da ya fitar a ranar Litinin, ya ce, Buharin tun lokacin da ya shiga ofis a shekarar 2015, bai taba umartar wani mutum da ya yi bore wa umarnin kotuna ba, ya yi imanin cewa demurudiyya ba za ta samu yadda ake bukata ba muddin babu doka.

 

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

“Kan halin da ake ciki na batun tsoffin kudade, akwai bukatar jama’a su sani shugaba Buhari bai yi komai wajen kawo cikas ga sashin shari’a ba.

 

“Bai taka burkin ko hana Antoni Janar da gwamnan CBN daga gudanar da ayyukansu da doka ya tadanar ba. Don haka babu wata shaida da za ta iya nuna cewa shi din ya hana mutanen biyu biyaya ga umarnin babban kotun.

 

“Shi dai shugaban kasa bayan ganawar da ya yi da Majalisar Kolin kasa. Ya umarci banki da ya tabbatar ya wadatar al’ummar kasa da takardun kudade da suke bukata, kuma babu wani abun da ya canza wannan matsayin nasa.

 

“Wannan kadai ya ishi al’umma su fahimci cewa shugaba Buhari na matukar mutunta umarnin kotuna.”

 

Sanarwar ta ce, hatta kesa-kesan da suka shafi cin hanci da rashawa, shugaban baya katsalandan wa harkar shari’a balle ma ya tsoma bakinsa domin yana barin kotuna su yi aikinsu yadda doka ya tanadar.

 

Garba Shehu ya ce, masu tashi haikan wajen ganin sun bata sunan Buhari da shafa masa kashin kaji na rashin biyayya ga kotu kai tsaye hakan rashin adalci muraran, “Domin babu wani umarnin kotu a kowace gaba da aka yi kai tsaye ga shi ‘Buhari’ a kashin kansa.”

 

“CBN bai da wani dalilin da zai ki biyayya wa umarnin kotu ya ce yana zaman jiran umarnin shugaban kasa,” Garba ya kara.

 

Buhari ya kuma karyata jita-jitan da wasu ke yi na cewa gwamamtinsa ta kawo tsare-tsaren da suka ruguza sashin tattalin arziki, yana mai cewa Babu wata gwamnatin da ta fito da tsare-tsare da kyawawan manufofin bunkasa tattalin arziki irin tasa gwamnatin.

Buhari
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Noma

Da Dumi-Dumi: CBN Ya Amince Da Ci Gaba Da Amfani Da Tsofaffin Takardun Naira

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.