• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bankin Duniya Da Hukumar Lamuni Ke Yi Wa Tsarin Ilimin Nijeriya Zagon-kasa – ASUU

by Sani Anwar and Sulaiman
7 months ago
in Labarai
0
Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani

World Bank on glass building. Mirrored sky and city modern facade. Global capital, business, finance, economy, banking and money concept 3D rendering animation.

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Kasa (ASUU), ta zargi Babban Bankin Duniya da kuma Hukumar Bayar da Lamuni ta Duniya (IMF) da yin zagon kasa, don lalata tsarin ilimin al’umma a Nijeriya.

 

Kungiyar ta kuma koka a kan jinkirin da aka samu wajen sake tattaunawa da gwamnatin tarayya a shekarar 2009, inda ta ce duk da cewa, an cimma yarjejeniya da gwamnatin tarayyar da dama, amma har yanzu ba a kammala tattaunawar da kungiyar ta ASUU da kuma gwamnatin ba.

  • Sin Ta Kafa Tsarin Ilimin Koyar Da Sana’o’i Mafi Girma A Duniya
  • Cire Tallafin Man Fetur Ya Kawo Ƙarshen Fasa-ƙwauri, in ji NSA

Shuugaban na ASUU, Farfesa Emmanuel Osodeke ne ya bayyana hakan ranar Talata a Abuja; yayin bikin ranar jaruman kungiyar ta 2024 zuwa 2025.

 

Labarai Masu Nasaba

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

Har ila yau, shugaban ya yi nadamar bayyana yadda lamarin ya kara dagulewa sakamakon aiwatar da tsarin da aka cimma na IPPIS a jami’o’in gwamnati, bayan da majalisar zartarwa ta tarayya ta bayyana shirin cire tsarin daga makarantun gaba da sakandire.

 

Osodeke ya kuma nuna damuwarsa, kan yadda har yanzu gwamnatin tarayya ke ci gaba da rike wa kungiyar albashi na wata uku da rabi; ba bisa ka’ida ba, baya ga wasu bashisshikan albashin da na karin girma da kuma alawus-alawus, wanda har yanzu ba ta biya ba.

 

Da yake yin karin haske a wajen taron, inda kungiyar ASUU ta ta karrama wadanda ta bayyana a matsayin “Tsoffin jarumanta wadanda har yanzu ke raye”, Osodeke ya yaba wa ‘ya’yan kungiyar na kasa baki-daya, bisa “Jajircewa da sadaukar da kai da suka yi wajen wajen tabbatar da wannan kungiya tamu, wanda ke da nasaba da ‘yantar da al’ummar Nijeriya har abada.”

 

Har wa yau, ya kuma bayyana cewa; kungiyar za ta bayar da tallafin karo karatu na digirin-digirgir (Ph.D) ga wasu mambobinta a jami’o’in gwamnati daban-daban na wannan kasa. Tallafin, zai kasance na Naira 500,000 ga duk wanda ya yi katarin samu, sannan za a bayar da shi ne bisa la’akari da shawarwarin da kwararru daga cikin mambobin suka bayar.

 

“’Yan’uwa, kamar a baya ma; bikin na bana na jaruman namu na gudana ne a daidai lokacin da muke ci gaba da fafutukar ganin an ceto jami’o’in gwamnatin Nijeriya daga halin kunci, wanda Babban Bankin Duniya (World Bank) da Hukumar Bayar da Lamuni ta Duniya (IMF) suka jefa su, wadanda yunkurinsu na ruguzawa ko binne tsarin jami’o’in bai yi nasara ba.

 

Wadanda aka karrama a wajen taron su ne; Farfesa T. Uzodinma Nwala; Farfesa Bright Ekuerhare; Farfesa Oye Oyediran; Mallam Bashir Kurfi; Farfesa The Name Ikiddeh; Mista S.A. Fadipe da kuma Farfesa Sola Olukunle.

 

Sauran sun hada da; Nasir Hussain; Tunde Oduleye; Farfesa Rasheed Abubakar; Akin Oyebode; Mustapha A. Danesi; A.T. Wins; and da kuma Peter Ozo-son.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Fashewar Gas Ta Jikkata Mutane, Ta Lalata Gidaje Da Motoci A Jibiya

Next Post

An Yi Garkuwa Da Sama Da ‘Yan Nijeriya 971 A Watan Oktoban 2024 – Rahoto

Related

Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

7 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

9 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

10 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

11 hours ago
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu
Labarai

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

13 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara
Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

14 hours ago
Next Post
Da Dumi-duminsa: ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Basarake A Ondo

An Yi Garkuwa Da Sama Da ‘Yan Nijeriya 971 A Watan Oktoban 2024 – Rahoto

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.