• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bankin Duniya Da Hukumar Lamuni Ke Yi Wa Tsarin Ilimin Nijeriya Zagon-kasa – ASUU

by Sani Anwar and Sulaiman
8 months ago
in Labarai
0
Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani

World Bank on glass building. Mirrored sky and city modern facade. Global capital, business, finance, economy, banking and money concept 3D rendering animation.

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Kasa (ASUU), ta zargi Babban Bankin Duniya da kuma Hukumar Bayar da Lamuni ta Duniya (IMF) da yin zagon kasa, don lalata tsarin ilimin al’umma a Nijeriya.

 

Kungiyar ta kuma koka a kan jinkirin da aka samu wajen sake tattaunawa da gwamnatin tarayya a shekarar 2009, inda ta ce duk da cewa, an cimma yarjejeniya da gwamnatin tarayyar da dama, amma har yanzu ba a kammala tattaunawar da kungiyar ta ASUU da kuma gwamnatin ba.

  • Sin Ta Kafa Tsarin Ilimin Koyar Da Sana’o’i Mafi Girma A Duniya
  • Cire Tallafin Man Fetur Ya Kawo Ƙarshen Fasa-ƙwauri, in ji NSA

Shuugaban na ASUU, Farfesa Emmanuel Osodeke ne ya bayyana hakan ranar Talata a Abuja; yayin bikin ranar jaruman kungiyar ta 2024 zuwa 2025.

 

Labarai Masu Nasaba

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har ila yau, shugaban ya yi nadamar bayyana yadda lamarin ya kara dagulewa sakamakon aiwatar da tsarin da aka cimma na IPPIS a jami’o’in gwamnati, bayan da majalisar zartarwa ta tarayya ta bayyana shirin cire tsarin daga makarantun gaba da sakandire.

 

Osodeke ya kuma nuna damuwarsa, kan yadda har yanzu gwamnatin tarayya ke ci gaba da rike wa kungiyar albashi na wata uku da rabi; ba bisa ka’ida ba, baya ga wasu bashisshikan albashin da na karin girma da kuma alawus-alawus, wanda har yanzu ba ta biya ba.

 

Da yake yin karin haske a wajen taron, inda kungiyar ASUU ta ta karrama wadanda ta bayyana a matsayin “Tsoffin jarumanta wadanda har yanzu ke raye”, Osodeke ya yaba wa ‘ya’yan kungiyar na kasa baki-daya, bisa “Jajircewa da sadaukar da kai da suka yi wajen wajen tabbatar da wannan kungiya tamu, wanda ke da nasaba da ‘yantar da al’ummar Nijeriya har abada.”

 

Har wa yau, ya kuma bayyana cewa; kungiyar za ta bayar da tallafin karo karatu na digirin-digirgir (Ph.D) ga wasu mambobinta a jami’o’in gwamnati daban-daban na wannan kasa. Tallafin, zai kasance na Naira 500,000 ga duk wanda ya yi katarin samu, sannan za a bayar da shi ne bisa la’akari da shawarwarin da kwararru daga cikin mambobin suka bayar.

 

“’Yan’uwa, kamar a baya ma; bikin na bana na jaruman namu na gudana ne a daidai lokacin da muke ci gaba da fafutukar ganin an ceto jami’o’in gwamnatin Nijeriya daga halin kunci, wanda Babban Bankin Duniya (World Bank) da Hukumar Bayar da Lamuni ta Duniya (IMF) suka jefa su, wadanda yunkurinsu na ruguzawa ko binne tsarin jami’o’in bai yi nasara ba.

 

Wadanda aka karrama a wajen taron su ne; Farfesa T. Uzodinma Nwala; Farfesa Bright Ekuerhare; Farfesa Oye Oyediran; Mallam Bashir Kurfi; Farfesa The Name Ikiddeh; Mista S.A. Fadipe da kuma Farfesa Sola Olukunle.

 

Sauran sun hada da; Nasir Hussain; Tunde Oduleye; Farfesa Rasheed Abubakar; Akin Oyebode; Mustapha A. Danesi; A.T. Wins; and da kuma Peter Ozo-son.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Fashewar Gas Ta Jikkata Mutane, Ta Lalata Gidaje Da Motoci A Jibiya

Next Post

An Yi Garkuwa Da Sama Da ‘Yan Nijeriya 971 A Watan Oktoban 2024 – Rahoto

Related

Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

10 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

10 hours ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)
Labarai

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

11 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

11 hours ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

14 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

15 hours ago
Next Post
Da Dumi-duminsa: ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Basarake A Ondo

An Yi Garkuwa Da Sama Da ‘Yan Nijeriya 971 A Watan Oktoban 2024 – Rahoto

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.