• English
  • Business News
Wednesday, October 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bankin Duniya Ya Yi Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Nijeriya Da Kashi 3.3 A 2024

by Bello Hamza
2 years ago
Bankin Duniya

Bankin Duniya ya yi a hasashen bunkasar tattalin arzikin Nijeriya a shekarar 2024 daga hasashen da ya yi na kashi 2.9 a watan Oktoba na shekarar da ta gabata zuwa kashi 3.3 a wannan shekara da kuma kashi 3.7 a shekarar 2025, kamar dai yadda rahotonsa na watan Janairun 2024 ya nuna.

Ana hasashen tattalin arzikin duniya zai yi kasa a karshen shekarar 2024, wannan kuma shi ne tafiyar hawainiyar Mfi girma da aka samu a cikin shekara 30, kamar dai yadda mujallar bankin duniya mai suna ‘Global Economic Prospects’ ta nuna.

  • Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Shekarar 2023
  • Kotun Koli Ta Tabbatar Da Zaben Alex Otti A Matsayin Gwamnan Abia

Bankin Duniyan ya yi wannan hasashen ne tare dda fatan tsare-tsaren tattalin arzikin da gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ke gudanarwa a kasa za su haifar da da mai ido. Duk da cewa, tana da tunanin za a samu koma bayan tattalin arziki a duniya, shekara uku a jere, kashi 2.4 kafin kuma ya koma kashi 2.7 a shekarar 2025.

Rahoton ya nuna cewa, za a samu bunkasar tattalin a rziki a wannan shekarar na kashi 3.3 zai kuma karu zuwa kashi 3.7 a shekarar 2025, wannan na faruwa ne saboda ganin matakan bunkasar tattalin arzikin na da gwamnati ke yin a kara bayyana.

“An yi hasashen ne da fatan tattalin arzikin kasa zai bunkasa tare da gudummawa da tallafin harkar aikin gona, gine-gine, da kuma kasuwanci. Za kuma a samu saukin hauhawar farashi saboda matsin da janye tallafin man fetur ya haifar zai ragu a hankali.

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

Rashin Abinci Mai Gina Jiki Barazana Ce Ga Lafiyar Al’umma – Gwamna Lawal

Haka kuma abubuwan da za su taimaka wajen bunkasar tattalin arzikin Nijeriya a wannan shekarar sun hada da fitar da wasu kayyakin da ake sarrafawa a gida zuwa kasashen waje da kuma sake fasallin farashin kayayyaki a hankali ta yadda al’uimma za su shiga saye da sayarwa don bunkasa tattalin arzikin su.

“An kuma samu bunkasa yanayin rayuwar al’umma, musamman yadda aka samu kwanciyar hankali a tafiyar da tsarin dimokradiyya a Nijeriya da ma nahiyar Afirka gaba daya”, in ji rahoton.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta
Da ɗumi-ɗuminsa

ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

October 22, 2025
Rashin Abinci Mai Gina Jiki Barazana Ce Ga Lafiyar Al’umma – Gwamna Lawal
Labarai

Rashin Abinci Mai Gina Jiki Barazana Ce Ga Lafiyar Al’umma – Gwamna Lawal

October 22, 2025
Majalisa Ta Amince Da Dokar Ɗaurin Rai Da Rai Ga Masu Yi Wa Ƙananan Yara Fyaɗe
Manyan Labarai

Majalisa Ta Amince Da Dokar Ɗaurin Rai Da Rai Ga Masu Yi Wa Ƙananan Yara Fyaɗe

October 22, 2025
Next Post
Manyan Abubuwan Da Sin Ta Fi Mayar Da Hankali A Kai A Shekarar 2023

Manyan Abubuwan Da Sin Ta Fi Mayar Da Hankali A Kai A Shekarar 2023

LABARAI MASU NASABA

Babaganaru Ya Zama Sabon Kocin Kano Pillars

Babaganaru Ya Zama Sabon Kocin Kano Pillars

October 22, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

October 22, 2025
ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

October 22, 2025
Rashin Abinci Mai Gina Jiki Barazana Ce Ga Lafiyar Al’umma – Gwamna Lawal

Rashin Abinci Mai Gina Jiki Barazana Ce Ga Lafiyar Al’umma – Gwamna Lawal

October 22, 2025
Majalisa Ta Amince Da Dokar Ɗaurin Rai Da Rai Ga Masu Yi Wa Ƙananan Yara Fyaɗe

Majalisa Ta Amince Da Dokar Ɗaurin Rai Da Rai Ga Masu Yi Wa Ƙananan Yara Fyaɗe

October 22, 2025
Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas

Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas

October 22, 2025
Gwamnoni Sun Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Fashewar Tankar Mai A Neja

Gwamnoni Sun Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Fashewar Tankar Mai A Neja

October 22, 2025
Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

October 21, 2025
Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

October 21, 2025
Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

October 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.