• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bankin Duniya Zai Amince Da Buƙatar Nijeriya Na Amsar Rancen Dala Miliyan 632

by Khalid Idris Doya
1 month ago
in Labarai
0
Bankin Duniya Zai Amince Da Buƙatar Nijeriya Na Amsar Rancen Dala Miliyan 632
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bankin Duniya ya shirya tsaf domin amincewa da sabon rokon cin bashin dala miliyan 632 da Nijeriya ke nema a daidai kabar da ake ta kukan yawan basukan da ke kan kasar ma sun yi yawa. 

Rancen wanda aka shirya ciwo shi domin taimaka wa bangarorin da suka hada da inganta sashin abinci mai gina jiki da samar da ilimi mai inganci a matakin farko.

  • Ofishin Siyasa Na Kwamitin Tsakiyar Jks Ya Kira Taron Nazarin Ayyukan Kiyaye Muhallin Halittu Da Sauransu
  • Dubban Jama’a Sun Sallaci Gawar Sheikh Idris Dutsen Tanshi

A bayanan da aka samu a shafin bankin dukiyar a ranar Lahadi, ya nuna cewa rancen ya kunshi na dala miliyan 80 da aka ware domin inganta sashin samar da abinci mai gina jikin dan’adam a Nijeriya a shiri na 2.0 da kuma wani rancen dala miliyan 552 da aka nema domin shiri mai hankoron samar da ingancin ilimi a matakin farko ga kowa.

Wannan matakin dai dukkan suna karkashin shirin babban bankin na taimaka wa Nijeriya a bangaren shirinta na samar da ci gaba da suke da manufar kyautata lafiya, ilimi da ci gaban jama’a.

Rancen ana sa ran za su taimaka wa kokarin gwamnatin tarayya na inganta samar da abinci mai gina jiki da kuma inganta samun damar ilimi mai inganci ga yara kanana a Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

A halin da ake ciki, tuni ma Bankin Duniya ya riga ya amince da lamunin dala miliyan 500 ga Nijeriya a ranar Juma’ar da ta gabata don tallafa wa shirin kasar na “Community Action for Resilience and Economic Stimulus Programme”.

Samun wannan rancen wani dama ce ga Nijeriya da zai taimaka mata wajen shawo kan matsalolin da suke bangaren tattalin arziki da inganta yanayin rayuwar jama’a, wadata kasa da abinci, da samar da range ga talakawa da kamfanoni.

Kazalika, a wani rancen da Nijeriya ta nema na dala miliyan 800 domin shirin ‘National Social Safety-Net Program Scale Up,’ Bankin Duniyan ya sake wa Nijeriya dala miliyan 315 daga cikin wannan adadin.

Tsawon kusan shekara, Nijeriya ba ta samu wani kudi daga Babban Bankin duniya ba a matsayin rance, tun bayan wanda ta ba ta a watan Disamban 2021. Na samu jinkirin sake kudaden ne sakamakon wasu batutuwa na damfara da aka gano a shirin.

Shugaban kasa Bola Tinubu ya kaddamar da shirin SSN wanda ke da manufar rabar da naira dubu 25,000 ga magidanta miliyan 15 na tsawon watanni uku domin yaki da fatara. Ma’aikatar kula da jin kai da yaki da talauci ne aka daura wa alhakin gudanar da shirin rancen dala miliyan 800 na Bankin Duniyan.

Har ila yau, gwamnatin tarayya ta dakatar da shirin tallafin kudi na (cash transfer programme) domin gudanar da bincike kan zarge-zargen almundahana da ke makale da shirin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DalaDuniya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnati Za Ta Dawo Da Sayar Wa Dangote Ɗanyen Mai Da Farashin Naira

Next Post

APC Ta Musanta Zargin Sauya Kashim Shettima A Zaɓen 2027

Related

Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?
Manyan Labarai

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

45 minutes ago
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 
Labarai

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

9 hours ago
Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe
Labarai

Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

10 hours ago
Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

12 hours ago
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya
Labarai

Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

13 hours ago
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar
Manyan Labarai

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

15 hours ago
Next Post
APC Ta Musanta Zargin Sauya Kashim Shettima A Zaɓen 2027

APC Ta Musanta Zargin Sauya Kashim Shettima A Zaɓen 2027

LABARAI MASU NASABA

Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

May 14, 2025
Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

May 13, 2025
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

May 13, 2025
Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

May 13, 2025
Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

May 13, 2025
Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

May 13, 2025
Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

May 13, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

May 13, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

May 13, 2025
An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.