ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bankin Duniya Zai Amince Da Buƙatar Nijeriya Na Amsar Rancen Dala Miliyan 632

by Khalid Idris Doya
1 year ago
Duniya

Bankin Duniya ya shirya tsaf domin amincewa da sabon rokon cin bashin dala miliyan 632 da Nijeriya ke nema a daidai kabar da ake ta kukan yawan basukan da ke kan kasar ma sun yi yawa. 

Rancen wanda aka shirya ciwo shi domin taimaka wa bangarorin da suka hada da inganta sashin abinci mai gina jiki da samar da ilimi mai inganci a matakin farko.

  • Ofishin Siyasa Na Kwamitin Tsakiyar Jks Ya Kira Taron Nazarin Ayyukan Kiyaye Muhallin Halittu Da Sauransu
  • Dubban Jama’a Sun Sallaci Gawar Sheikh Idris Dutsen Tanshi

A bayanan da aka samu a shafin bankin dukiyar a ranar Lahadi, ya nuna cewa rancen ya kunshi na dala miliyan 80 da aka ware domin inganta sashin samar da abinci mai gina jikin dan’adam a Nijeriya a shiri na 2.0 da kuma wani rancen dala miliyan 552 da aka nema domin shiri mai hankoron samar da ingancin ilimi a matakin farko ga kowa.

ADVERTISEMENT

Wannan matakin dai dukkan suna karkashin shirin babban bankin na taimaka wa Nijeriya a bangaren shirinta na samar da ci gaba da suke da manufar kyautata lafiya, ilimi da ci gaban jama’a.

Rancen ana sa ran za su taimaka wa kokarin gwamnatin tarayya na inganta samar da abinci mai gina jiki da kuma inganta samun damar ilimi mai inganci ga yara kanana a Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

A halin da ake ciki, tuni ma Bankin Duniya ya riga ya amince da lamunin dala miliyan 500 ga Nijeriya a ranar Juma’ar da ta gabata don tallafa wa shirin kasar na “Community Action for Resilience and Economic Stimulus Programme”.

Samun wannan rancen wani dama ce ga Nijeriya da zai taimaka mata wajen shawo kan matsalolin da suke bangaren tattalin arziki da inganta yanayin rayuwar jama’a, wadata kasa da abinci, da samar da range ga talakawa da kamfanoni.

Kazalika, a wani rancen da Nijeriya ta nema na dala miliyan 800 domin shirin ‘National Social Safety-Net Program Scale Up,’ Bankin Duniyan ya sake wa Nijeriya dala miliyan 315 daga cikin wannan adadin.

Tsawon kusan shekara, Nijeriya ba ta samu wani kudi daga Babban Bankin duniya ba a matsayin rance, tun bayan wanda ta ba ta a watan Disamban 2021. Na samu jinkirin sake kudaden ne sakamakon wasu batutuwa na damfara da aka gano a shirin.

Shugaban kasa Bola Tinubu ya kaddamar da shirin SSN wanda ke da manufar rabar da naira dubu 25,000 ga magidanta miliyan 15 na tsawon watanni uku domin yaki da fatara. Ma’aikatar kula da jin kai da yaki da talauci ne aka daura wa alhakin gudanar da shirin rancen dala miliyan 800 na Bankin Duniyan.

Har ila yau, gwamnatin tarayya ta dakatar da shirin tallafin kudi na (cash transfer programme) domin gudanar da bincike kan zarge-zargen almundahana da ke makale da shirin.

Duniya
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
APC Ta Musanta Zargin Sauya Kashim Shettima A Zaɓen 2027

APC Ta Musanta Zargin Sauya Kashim Shettima A Zaɓen 2027

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.