• English
  • Business News
Thursday, June 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

by Hussein Yero and Sulaiman
1 month ago
in Labarai
0
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Dauda Lawal ya raba wasu motocin zirga-zirga ga rukunonin jami’an tsaron da ke aiki a jihar Zamfara.

Bikin ƙaddamar da rabon motocin tsaron, tare da motocin sufurin na ‘Zamfara Mass Transit’ ya gudana ne a filin Kasuwar Duniya da ke Gusau a yau Talatar nan.

  • Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe
  • Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

A cikin wata sanarwa da Kakakin Gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya sanya wa hannu yau a Gusau, ya bayyana cewa Babban Kwamandan Hukumar tsaro ta NSCDC, Dr. Ahmed Abubakar Audi, mni, OFR ne ya zama babban baƙo a wajen bikin.

Sanarwar ta Sulaiman ta ci gaba da bayyana cewa, gwamnatin jihar Zamfara ta samar da motocin aiki guda 140 ga Hukumomin tsaro, wanda ke tabbatar da cewa har yanzu samar da tsaro ne babban abin da gwamnatin ta fi ba fifiko.

Cikin jwabin sa a wurin bikin, Gwamna Dauda Lawal ya bayyana cewa gwamnatin sa ta kasance tana gaggawar bayar da kulawa da gudumawa ga jami’an tsaron da ke aiki a jihar.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Gurfanar Da Natasha A Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Akpabio Da Yahaya Bello

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Namadi Sambo Ya Karyata Sauya Sheƙa Zuwa APC

Zamfara

Ya ce, “Samar da motocin aiki ga jami’an tsaron zai bayar da ci gaba wajen sawwaƙa masu zirga-zirga, kai ɗauki a kan lokaci da ƙara ƙarfafa masu gwiwa wajen samar da tsaro da bin doka da oda.

“Wannan taro na yau, wani ci gaba ne na ƙoƙarin gwamnatina wajen ƙarfagawa, tare da inganta ayyukan jami’an tsaron da ke aiki a duk faɗin jihar.

“Wannan kuma yana ɗamfare ne da alƙawuran da muka yi, tare da jajircewar mu wajen samar da duk abin da za mu iya don tunkarar dukkan nau’o’in rashin tsaro, samar da zaman lafiya, kare rayuka da dukiyar jama’ar jihar mu.

“Wannan ƙoƙari namu yana ƙara nuna hobbasan gwamnatin mu wajen ƙarfafa wa jami’an tsaron mu don su samu sauƙin samar da tsaron rayuka da dukiyar al’ummar mu.

“Muna sane da muhimmancin ayyukan su wajen tabbatar da bin doka da oda don a samu cigababbiyar jihar Zamfara da ma ƙasa baki ɗaya.

“Saboda haka gwamnatina ta yi tsayin-daka wajen ganin an samar wa da jami’an tsaron nan, da duk goyon baya don su samu damar gudanar da ayyukan su cikin nasara.

“Ta bangare mu, mun kafa jami’an tsaron mu na kan mu, waɗanda muka sanya wa suna Jami’an Kare Al’ummar mu, Askarawan Zamfara, wato ‘Community Protection Guards.’ Mun yi niyyar tallafa wa ƙoƙarin ku, mu yi musayar ra’ayi, mu jawo al’ummar mu don kare ƙasar mu.

“A wannan taro namu na yau, mun shirya raba motoci guda 140 sabbi dal ga rukunonin jami’an tsaron mu da ke aiki a jihar nan. Waɗanda suka haɗa da A-kori kura mai gida biyu da motocin tsaro na Buffalo, duk mun samar da su ne don ƙarfafa wa jami’an tsaron da suka amfana.”

Gwamnan ya ci gaba da cewa gwamnatin sa ta samar da motocin ba-bas sabbi guda 50 don inganta harkar sufuri a jihar.

“Wannan yana daga cikin tsarin mu na inganta harkar sufurin cikin gida da masu tafiya zuwa wajen jihar.

“Mun samar da kyakkyawan tsarin da zai tabbatar da kula da motocin, da kuma hana almubazzarancin da kuɗin da ake tarawa a harkar.

Zamfara

“Akwai na’urorin da aka sanya wa waɗannan motoci, waɗanda za nuna inda mota ta ke a kowane lokaci, an kuma sanya internet a cikin su domin fasinjoji.

“Kafin in kammala jawabina, zan girmama sadaukar da ran da Askarawan mu suka yi, waɗanda suka rasa rayukan su wajen kare martabar ƙasar mu, tare da iyalan da suka bari. Muna tuna ku a kowane lokaci, kuma muna girmama sadaukarwar ku.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

Next Post

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Gurfanar Da Natasha A Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Akpabio Da Yahaya Bello
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Gurfanar Da Natasha A Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Akpabio Da Yahaya Bello

3 hours ago
Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Namadi Sambo Ya Karyata Sauya Sheƙa Zuwa APC
Manyan Labarai

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Namadi Sambo Ya Karyata Sauya Sheƙa Zuwa APC

3 hours ago
Masarautar Gaya Ta Ƙwace Sarautar Wazirin Gaya Da Ta Bai Wa Tsohon Sakataren Gwamnatin Kano
Labarai

Masarautar Gaya Ta Ƙwace Sarautar Wazirin Gaya Da Ta Bai Wa Tsohon Sakataren Gwamnatin Kano

5 hours ago
Gwamnonin APC Sun Nemi Tinubu Ya Ƙirkiri ‘Yansandan Jihohi Don Yaƙar Matsalar Tsaro
Manyan Labarai

Gwamnonin APC Sun Nemi Tinubu Ya Ƙirkiri ‘Yansandan Jihohi Don Yaƙar Matsalar Tsaro

6 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Kebbi, Sun Kashe Mutane Da Dama
Manyan Labarai

Lakurawa Sun Sanya Dokar Hana Sayar Da Shanu A Kebbi

9 hours ago
Kawayen amarya
Manyan Labarai

An Kashe Wasu ‘Yan Bindiga 12, An Kwato Makamai A Katsina

18 hours ago
Next Post
Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Gurfanar Da Natasha A Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Akpabio Da Yahaya Bello

Gwamnatin Tarayya Ta Gurfanar Da Natasha A Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Akpabio Da Yahaya Bello

June 19, 2025
Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Namadi Sambo Ya Karyata Sauya Sheƙa Zuwa APC

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Namadi Sambo Ya Karyata Sauya Sheƙa Zuwa APC

June 19, 2025
Masarautar Gaya Ta Ƙwace Sarautar Wazirin Gaya Da Ta Bai Wa Tsohon Sakataren Gwamnatin Kano

Masarautar Gaya Ta Ƙwace Sarautar Wazirin Gaya Da Ta Bai Wa Tsohon Sakataren Gwamnatin Kano

June 19, 2025
Gwamnonin APC Sun Nemi Tinubu Ya Ƙirkiri ‘Yansandan Jihohi Don Yaƙar Matsalar Tsaro

Gwamnonin APC Sun Nemi Tinubu Ya Ƙirkiri ‘Yansandan Jihohi Don Yaƙar Matsalar Tsaro

June 19, 2025
Ba Za Mu Yarda A Yi Mana Ƙarfa-ƙarfa Ba – Ayatollah Ya Gargaɗi Amurka

Ba Za Mu Yarda A Yi Mana Ƙarfa-ƙarfa Ba – Ayatollah Ya Gargaɗi Amurka

June 19, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Kebbi, Sun Kashe Mutane Da Dama

Lakurawa Sun Sanya Dokar Hana Sayar Da Shanu A Kebbi

June 19, 2025
Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya

Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya

June 18, 2025
Kawayen amarya

An Kashe Wasu ‘Yan Bindiga 12, An Kwato Makamai A Katsina

June 18, 2025
Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi

Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi

June 18, 2025
WTO Na Darajanta Tallafin Kasar Sin a Bangaren Cinikayya Ga Kasashe Masu Tasowa

WTO Na Darajanta Tallafin Kasar Sin a Bangaren Cinikayya Ga Kasashe Masu Tasowa

June 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.