• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Barazanar Kai Hari Abuja: Buhari Ya Bukaci ‘Yan Nijeriya Su Kwantar Da Hankalinsu

bySadiq
3 years ago
Buhari

Shugaban kasa Muhammadu ya shawarci jami’an tsaron kasar da daukacin al’ummar kasar da su ci gaba da yin taka-tsantsan da harkokin tsaro, kuma ya bukaci kowa ya kwantar da hankalinsa. 

Ya bukaci ‘yan kasar da su kwantar da hankalinsu, inda ya ce akwai sauye-sauye da aka samu kan sha’anin tsaro.

  • Ta Yaya Za A Kubutar Da Kananan Yaran Amurka Daga Harbe-harben Bindiga
  • Malaman Jami’o’i Sun Koma Bakin Aiki Cikin Yunwa – Shugaban ASUU

A cewar wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasa, Garba Shehu ya fitar, shugaban kasar ya ce Nijeriya ba ta bar baya da kura ba a cikin jerin barazanar ta’addanci a cikin shawarwarin da ofishin jakadancin Amurka ya bayar.

Ya ce shawarwarin tafiye-tafiye na Birtaniya da Amurka sun kuma lura da yiwuwar kai hare-haren ta’addanci a yawancin kasashen yammacin Turai.

Hakika, Buhari ya ce shawarar Birtaniya da Amurka ga ‘yan kasarsu na yin balaguro zuwa kasashensu na dauke da wannan gargadin.

LABARAI MASU NASABA

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

Abin takaici, ta’addanci gaskiya ne a duniya. Sai dai ya ce hakan ba yana nufin za a kai hari Abuja ba.

“Tun daga harin da aka kai gidan yarin Kuje a watan Yuli, an karfafa matakan tsaro a babban birnin tarayya Abuja da kewaye.

Akwai sa ido da katse hanyoyin sadarwar ‘yan ta’adda don tabbatar da dakile kowace irin barazana.

“Ana dakile hare-hare. Jami’an tsaro suna aiki don kawar da barazana da kiyaye lafiyar ‘yan kasa – yawancin ayyukansu ba a gani saboda kusan a boye suke.

“Tsaron ‘yan Nijeriya shi ne babban fifikon gwamnati. Jami’an tsaro suna aiki ba dare ba rana don kiyaye kowace irin barna,” in ji shi.

Shugaban ya ba da tabbacin cewa gwamnati na kan gaba a harkar tsaro a kasar.

Ya kuma kara da cewa, ‘yansanda da sauran hukumomin tsaro suna kokari wajen tunkarar lamarin, kamar yadda ya tabbata daga yadda akasarin abokan huldar Nineriya, ciki har da hukumomin Majalisar Dinkin Duniya.

Shugaba Buhari ya ya bai wa sojoji da sauran jami’an tsaro kan yadda aka samu sauyin kan harkar tsaron kasar nan, ya kuma ba da umarnin a kara daukar matakan rigakafi kuma kada a yi kasa a gwiwa a lokacin bukukuwan da ke tafe.

Shugaba Buhari ya bayyana kwarin gwiwarsa na ganin yadda sojoji da sauran jami’an tsaro da na leken asiri ke yi tare da goyon bayan fararen hula, ya ce al’ummar kasar za su yi nasara a kan kalubalen da suke fuskanta a halin yanzu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo
Manyan Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025
Next Post
Xi Ya Bukaci A Yi Kokari Cikin Hadin Kai Wajen Cimma Burikan Babban Taron Wakilan JKS

Xi Ya Bukaci A Yi Kokari Cikin Hadin Kai Wajen Cimma Burikan Babban Taron Wakilan JKS

LABARAI MASU NASABA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version