• English
  • Business News
Tuesday, June 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Basukan Da Suka Yi Wa Nijeriya Katutu Ke Hana Ta Ci Gaba –IMF

by Abubakar Abba
8 months ago
in Tattalin Arziki
0
Basukan Da Suka Yi Wa Nijeriya Katutu Ke Hana Ta Ci Gaba –IMF
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Asusun lamuni na duniya IMF ya ce, Nijeriya kachokam na biyan basussuka ne da kudaden shigar da taka samu.

A cewar, asusun hakan ne ke janyo rashin samar da kudaden da za a yi amfani da su, wajen gudanar da dimbin ayyukan bunkasa kasa.

  • CMG Ta Gabatar Da Shirye-Shiryen Talabijin A Peru
  • MDD Za Ta Yi Duk Mai Yiwuwa Wajen Taimaka Wa Nijeriya Kawo Karshen Talauci

Babban Jami’i a sashen tsare-tsare na asusun Dabide Furceri ne ya sanar da hakan a taron manema labarai.

Furceri ya bayyan haka ne, a yayin taron hadaka a tsakanin asusun da bankin duniya da ake ci gaba da yin a karshen shekara a birnin Washington DC.

Kazalika, ya jaddada cewa, akwai matukar bukatar Nijeriya ta kara kirkiro da sabbin dabarun samarwa da kanta kudaden shiga, musamman domin ta rage wa kanta nauyi.

Labarai Masu Nasaba

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

A cewarsa, basussukan da Nijeriya ke biya daga kudaden shigar da take samu, sun kai yawan kashi 60.

Furceri ya ci gaba da cewa, hakan ya hana gwamnatin kasar, samun damar zuba hannun jari a cikin shirye-shiryenta na inganta rayuwar ‘yan kasar da kuma a fannin tattalin arzikin kasar.

Sai dai, ya yi nuni da cewa, an samu raguwa a kan biyan basussukan da kudin shigar wanda ya ragu daga kash 100, zuwa kashi 60.

Ya bayar da shawarar cewa, kamar kasashe irin Nijeriya, idan har za ta iya habaka kudaden shiggar da take samu, hakan zai bata damar kebe wasu kudaden shigar da kuma ware wadanda, za ta yi amfani da su domin biyan basussukan.

Ya sanar da cewa, yana da kyau Nijeriya ta kara mayar da hankali wajen kara haraji domin ta kara samarwa da kanta kudaden shiga, musamman ta hanyar samar da tsarin bin ka’ida ta yin gaskiya a fannin tara kudin shigar.

Bugu da kari, bisa wani rahoton da sashen sa ido na asusun IMF ya fitar a makon da ya gabata ya yi hasashen cewa, a yanzu Nijeriya matsayin da take biya, ya kai kashi 50.7.

Sai dai, Babban Jami’i ya bayyana cewa, ana sa ran biyan bashin zai ragu da kashi, 49.6 a shekarar 2025.

Rahoton ya bayyana cewa, basussukan sun hada da wasu takardun kudi daga babban bankin Nijeriya CBN da kuma wasu kadarori daga hukumar kula da kadarori ta kasa (AMCN).

Kazalika, rahoton ya sanar da cwa, bisa wani karin hasashen da aka yi ya nuna cewa, bashin zai kara raguwa zuwa kashi 48.5 a 2026, inda kuma zai kara raguwa zuwa kashi 48.2 a 2027.

Har ila yau, rahoton ya ci gaba da cewa, sai dai, za a samu dan karin da zai kashi 48.8 a 2028 da kuma zuwa kashi 49.1 a 2029.

Asusun na ya kuma bayar da shawarci gwamnatin tarayya da ta samar da hanyoyin da za a rage illar hauhawan farashin kaya da kuma kalubalen muhalli da marasa karfi ke fuskanta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BasukaIMFNijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kamfanin Simiti Na Dangote Ya Tallafa Wa Gidan Marayu Da Abinci A Lakwaja

Next Post

Yadda Barayin Amfanin Gona Ke Kassara Manoma

Related

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

1 week ago
Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island
Tattalin Arziki

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

2 weeks ago
Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata

4 weeks ago
Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Ce Za A Kammala Aikin NSWP A Zango Na Daya A 2026

2 months ago
Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar
Tattalin Arziki

Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar

2 months ago
Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC

2 months ago
Next Post
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Yadda Barayin Amfanin Gona Ke Kassara Manoma

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’an Tsaro 4 Da Manoma A Katsina

‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’an Tsaro 4 Da Manoma A Katsina

June 17, 2025
Matatar Mai ta Haifa Ta Dakatar Da Ayyukanta Bayan Harin Iran

Matatar Mai ta Haifa Ta Dakatar Da Ayyukanta Bayan Harin Iran

June 17, 2025
Sirikin Buhari Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Kaduna

Dalilin Mara Wa Tinubu Baya Ba Tare da Ambaton Shettima Ba – Shugaban APC Na Arewa Maso Gabas

June 17, 2025
Sabon Shirin Gwamnatin Katsina: Za A Fara Sauya Tunanin Tubabbun ‘Yan Bindiga

Sabon Shirin Gwamnatin Katsina: Za A Fara Sauya Tunanin Tubabbun ‘Yan Bindiga

June 17, 2025
‘Yansanda Sun Kama Matasa 51 da Ake Zargi Da Faɗan Daba A Kano

‘Yansanda Sun Kama Matasa 51 da Ake Zargi Da Faɗan Daba A Kano

June 17, 2025
Hada-hadar Tattalin Arzikin Sin Ta Gudana Bisa Daidaito A Watan Mayu

Hada-hadar Tattalin Arzikin Sin Ta Gudana Bisa Daidaito A Watan Mayu

June 16, 2025
Ministan Waje: Kwakkwaran Zumunci Da Ake Sadawa Da Sin Ya Yi Tasiri Mai Kyau Ga Al’ummar Rwanda

Ministan Waje: Kwakkwaran Zumunci Da Ake Sadawa Da Sin Ya Yi Tasiri Mai Kyau Ga Al’ummar Rwanda

June 16, 2025
Sarkin Musulmi Ya Nuna Baƙin Ciki Kan Kisan Kiyashi A Binuwe

Sarkin Musulmi Ya Nuna Baƙin Ciki Kan Kisan Kiyashi A Binuwe

June 16, 2025
Hada-hadar Tattalin Arzikin Sin Ta Gudana Bisa Daidaito A Watan Mayu

Hada-hadar Tattalin Arzikin Sin Ta Gudana Bisa Daidaito A Watan Mayu

June 16, 2025
Sin Ta Fatattaki Laifukan Zamba Ta Shafin Intanet 294,000 A Bara

Sin Ta Fatattaki Laifukan Zamba Ta Shafin Intanet 294,000 A Bara

June 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.