• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Basukan Da Suka Yi Wa Nijeriya Katutu Ke Hana Ta Ci Gaba –IMF

by Abubakar Abba
11 months ago
in Tattalin Arziki
0
Basukan Da Suka Yi Wa Nijeriya Katutu Ke Hana Ta Ci Gaba –IMF
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Asusun lamuni na duniya IMF ya ce, Nijeriya kachokam na biyan basussuka ne da kudaden shigar da taka samu.

A cewar, asusun hakan ne ke janyo rashin samar da kudaden da za a yi amfani da su, wajen gudanar da dimbin ayyukan bunkasa kasa.

  • CMG Ta Gabatar Da Shirye-Shiryen Talabijin A Peru
  • MDD Za Ta Yi Duk Mai Yiwuwa Wajen Taimaka Wa Nijeriya Kawo Karshen Talauci

Babban Jami’i a sashen tsare-tsare na asusun Dabide Furceri ne ya sanar da hakan a taron manema labarai.

Furceri ya bayyan haka ne, a yayin taron hadaka a tsakanin asusun da bankin duniya da ake ci gaba da yin a karshen shekara a birnin Washington DC.

Kazalika, ya jaddada cewa, akwai matukar bukatar Nijeriya ta kara kirkiro da sabbin dabarun samarwa da kanta kudaden shiga, musamman domin ta rage wa kanta nauyi.

Labarai Masu Nasaba

Bayan Shekara 20 Nijeriya Ta Sake Dawo Da Tsarin Bayar Da Hayar Kananan Jiragen Sama

Tashoshin Jiragen Ruwa Sun Samar Da Kashi 19.6 Na Fitar Da Kayan Da Ba Su Shafi Mai Ba—Dantsoho

A cewarsa, basussukan da Nijeriya ke biya daga kudaden shigar da take samu, sun kai yawan kashi 60.

Furceri ya ci gaba da cewa, hakan ya hana gwamnatin kasar, samun damar zuba hannun jari a cikin shirye-shiryenta na inganta rayuwar ‘yan kasar da kuma a fannin tattalin arzikin kasar.

Sai dai, ya yi nuni da cewa, an samu raguwa a kan biyan basussukan da kudin shigar wanda ya ragu daga kash 100, zuwa kashi 60.

Ya bayar da shawarar cewa, kamar kasashe irin Nijeriya, idan har za ta iya habaka kudaden shiggar da take samu, hakan zai bata damar kebe wasu kudaden shigar da kuma ware wadanda, za ta yi amfani da su domin biyan basussukan.

Ya sanar da cewa, yana da kyau Nijeriya ta kara mayar da hankali wajen kara haraji domin ta kara samarwa da kanta kudaden shiga, musamman ta hanyar samar da tsarin bin ka’ida ta yin gaskiya a fannin tara kudin shigar.

Bugu da kari, bisa wani rahoton da sashen sa ido na asusun IMF ya fitar a makon da ya gabata ya yi hasashen cewa, a yanzu Nijeriya matsayin da take biya, ya kai kashi 50.7.

Sai dai, Babban Jami’i ya bayyana cewa, ana sa ran biyan bashin zai ragu da kashi, 49.6 a shekarar 2025.

Rahoton ya bayyana cewa, basussukan sun hada da wasu takardun kudi daga babban bankin Nijeriya CBN da kuma wasu kadarori daga hukumar kula da kadarori ta kasa (AMCN).

Kazalika, rahoton ya sanar da cwa, bisa wani karin hasashen da aka yi ya nuna cewa, bashin zai kara raguwa zuwa kashi 48.5 a 2026, inda kuma zai kara raguwa zuwa kashi 48.2 a 2027.

Har ila yau, rahoton ya ci gaba da cewa, sai dai, za a samu dan karin da zai kashi 48.8 a 2028 da kuma zuwa kashi 49.1 a 2029.

Asusun na ya kuma bayar da shawarci gwamnatin tarayya da ta samar da hanyoyin da za a rage illar hauhawan farashin kaya da kuma kalubalen muhalli da marasa karfi ke fuskanta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BasukaIMFNijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kamfanin Simiti Na Dangote Ya Tallafa Wa Gidan Marayu Da Abinci A Lakwaja

Next Post

Yadda Barayin Amfanin Gona Ke Kassara Manoma

Related

Bayan Shekara 20 Nijeriya Ta Sake Dawo Da Tsarin Bayar Da Hayar Kananan Jiragen Sama
Tattalin Arziki

Bayan Shekara 20 Nijeriya Ta Sake Dawo Da Tsarin Bayar Da Hayar Kananan Jiragen Sama

2 days ago
Tashoshin Jiragen Ruwa Sun Samar Da Kashi 19.6 Na Fitar Da Kayan Da Ba Su Shafi Mai Ba—Dantsoho
Tattalin Arziki

Tashoshin Jiragen Ruwa Sun Samar Da Kashi 19.6 Na Fitar Da Kayan Da Ba Su Shafi Mai Ba—Dantsoho

2 days ago
Majalisar Wakilai Za Ta Sasanta Dangote Da NUPENG
Tattalin Arziki

Majalisar Wakilai Za Ta Sasanta Dangote Da NUPENG

1 week ago
Yadda Sauye-Sauyen Da Aka Yi A Fannin Mai Da Iskar Gas Suka Samar Da Gagarumin Ci Gaba A Wannan Shekarar
Tattalin Arziki

Yadda Sauye-Sauyen Da Aka Yi A Fannin Mai Da Iskar Gas Suka Samar Da Gagarumin Ci Gaba A Wannan Shekarar

1 week ago
Manyan Motoci 2,000 A Kullum Ke Zirga-zirga A Tashoshin Jiragen Ruwa Na Jihar Legas —Rahoto
Tattalin Arziki

Manyan Motoci 2,000 A Kullum Ke Zirga-zirga A Tashoshin Jiragen Ruwa Na Jihar Legas —Rahoto

1 week ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Tattalin Arziki

NPA Ta Fara Aiki Da Sabon Tsarin ETO A Tashar Apapa

3 weeks ago
Next Post
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Yadda Barayin Amfanin Gona Ke Kassara Manoma

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.