ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, September 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Basukan Da Suka Yi Wa Nijeriya Katutu Ke Hana Ta Ci Gaba –IMF

by Abubakar Abba
2 years ago
IMF

Asusun lamuni na duniya IMF ya ce, Nijeriya kachokam na biyan basussuka ne da kudaden shigar da taka samu.

A cewar, asusun hakan ne ke janyo rashin samar da kudaden da za a yi amfani da su, wajen gudanar da dimbin ayyukan bunkasa kasa.

  • CMG Ta Gabatar Da Shirye-Shiryen Talabijin A Peru
  • MDD Za Ta Yi Duk Mai Yiwuwa Wajen Taimaka Wa Nijeriya Kawo Karshen Talauci

Babban Jami’i a sashen tsare-tsare na asusun Dabide Furceri ne ya sanar da hakan a taron manema labarai.

ADVERTISEMENT

Furceri ya bayyan haka ne, a yayin taron hadaka a tsakanin asusun da bankin duniya da ake ci gaba da yin a karshen shekara a birnin Washington DC.

Kazalika, ya jaddada cewa, akwai matukar bukatar Nijeriya ta kara kirkiro da sabbin dabarun samarwa da kanta kudaden shiga, musamman domin ta rage wa kanta nauyi.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Taron Bikin Maulidi Ya Gudana A Unguwar Mile 12 A Legas

NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba

A cewarsa, basussukan da Nijeriya ke biya daga kudaden shigar da take samu, sun kai yawan kashi 60.

Furceri ya ci gaba da cewa, hakan ya hana gwamnatin kasar, samun damar zuba hannun jari a cikin shirye-shiryenta na inganta rayuwar ‘yan kasar da kuma a fannin tattalin arzikin kasar.

Sai dai, ya yi nuni da cewa, an samu raguwa a kan biyan basussukan da kudin shigar wanda ya ragu daga kash 100, zuwa kashi 60.

Ya bayar da shawarar cewa, kamar kasashe irin Nijeriya, idan har za ta iya habaka kudaden shiggar da take samu, hakan zai bata damar kebe wasu kudaden shigar da kuma ware wadanda, za ta yi amfani da su domin biyan basussukan.

Ya sanar da cewa, yana da kyau Nijeriya ta kara mayar da hankali wajen kara haraji domin ta kara samarwa da kanta kudaden shiga, musamman ta hanyar samar da tsarin bin ka’ida ta yin gaskiya a fannin tara kudin shigar.

Bugu da kari, bisa wani rahoton da sashen sa ido na asusun IMF ya fitar a makon da ya gabata ya yi hasashen cewa, a yanzu Nijeriya matsayin da take biya, ya kai kashi 50.7.

Sai dai, Babban Jami’i ya bayyana cewa, ana sa ran biyan bashin zai ragu da kashi, 49.6 a shekarar 2025.

Rahoton ya bayyana cewa, basussukan sun hada da wasu takardun kudi daga babban bankin Nijeriya CBN da kuma wasu kadarori daga hukumar kula da kadarori ta kasa (AMCN).

Kazalika, rahoton ya sanar da cwa, bisa wani karin hasashen da aka yi ya nuna cewa, bashin zai kara raguwa zuwa kashi 48.5 a 2026, inda kuma zai kara raguwa zuwa kashi 48.2 a 2027.

Har ila yau, rahoton ya ci gaba da cewa, sai dai, za a samu dan karin da zai kashi 48.8 a 2028 da kuma zuwa kashi 49.1 a 2029.

Asusun na ya kuma bayar da shawarci gwamnatin tarayya da ta samar da hanyoyin da za a rage illar hauhawan farashin kaya da kuma kalubalen muhalli da marasa karfi ke fuskanta.

IMF
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Yadda Taron Bikin Maulidi Ya Gudana A Unguwar Mile 12 A Legas
Tattalin Arziki

Yadda Taron Bikin Maulidi Ya Gudana A Unguwar Mile 12 A Legas

September 4, 2026
NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
Tattalin Arziki

NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba

September 4, 2026
NPA Ta Tabbatar Da Maido Da Manyan Kayan Aikin Hukumar Wuta Ta Neja Delta —Babbar Manaja
Tattalin Arziki

NPA Ta Tabbatar Da Maido Da Manyan Kayan Aikin Hukumar Wuta Ta Neja Delta —Babbar Manaja

August 28, 2026
Next Post
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Yadda Barayin Amfanin Gona Ke Kassara Manoma

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Nuna Rashin Jin Dadinta Ga Italiya Da Tarayyar Turai Kan Ziyarar Jami’ar DPP

Sin Ta Nuna Rashin Jin Dadinta Ga Italiya Da Tarayyar Turai Kan Ziyarar Jami’ar DPP

September 11, 2026
Sin Tana Son Cin Moriya Tare Da Sassan Duniya A Fannin Kirkire-kirkire

Sin Tana Son Cin Moriya Tare Da Sassan Duniya A Fannin Kirkire-kirkire

September 11, 2026
Sin Da Indiya Na Shirye-shiryen Ganawar Xi Da Modi

Sin Da Indiya Na Shirye-shiryen Ganawar Xi Da Modi

September 11, 2026
Hadin Gwiwar Hada-Hadar Ba Da Hidima Tsakanin Sin Da Afirka Na Karfafa Karfin Afirka

Hadin Gwiwar Hada-Hadar Ba Da Hidima Tsakanin Sin Da Afirka Na Karfafa Karfin Afirka

September 11, 2026
Zaben 2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Bayyana Shirinsu Yayin Da INEC Ta Fitar Da Jawalin Zabe

Dalilan Da Ya Sa Jam’iyyun Siyasa Suka Jinkirta Ƙaddamar Da Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen

September 11, 2026
Nazarin CGTN: Kungiyar BRICS Tana Kara Taka Rawar Gani A Harkokin Duniya

Nazarin CGTN: Kungiyar BRICS Tana Kara Taka Rawar Gani A Harkokin Duniya

September 11, 2026
Za A Ci ’Yan Siyasa Masu Kalaman Ɓatanci Tarar Miliyan 10 Da Ɗaurin Watanni 12 — INEC

2027: A Karon Farko INEC Za Ta Ƙaddamar Da Na’urar Bibiyar Zaɓen Nijeriya

September 11, 2026
Me Ya Sa Kamfanonin Amurka Ke Kyautata Zato Ga Sabuwar Damar Sin?

Me Ya Sa Kamfanonin Amurka Ke Kyautata Zato Ga Sabuwar Damar Sin?

September 11, 2026
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Gwamnati Ta Shekarar 2026  Mrs Zubaida Umar

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Gwamnati Ta Shekarar 2026 Mrs Zubaida Umar

September 11, 2026
Sin Ta Kafa Manufar Shiga Sahun Manyan Kasashen Dake Da Karfi A Harkar Kera Motoci A Duniya Nan Da Shekarar 2030

Sin Ta Kafa Manufar Shiga Sahun Manyan Kasashen Dake Da Karfi A Harkar Kera Motoci A Duniya Nan Da Shekarar 2030

September 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.