• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Batun Daurarru 3,298 Masu Jiran Hukuncin Kisa A Nijeriya

by Abdulrazaq Yahuza
2 years ago
in Labarai
0
Daurarru
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Batun cunkoson Gidajen Gyara Hali a fadin Nijeriya na ci gaba da zama cikin abubuwan tattaunawa a wurare da dama na harkokin al’umma a fadin kasar nan. Ga wadanda basu san cikakken halin da gidajen yarin suke ciki ba, har yanzu su na nan a halin da turawan mulkin mallaka suka samar da su a shekarun baya kafin su koma kasashen su da sunan bamu ‘yancin kai. Chanza sunan su daga yadda aka san su a da tunda farko na ‘Nigerian Prison Serbice (NPS)’ zuwa ‘Nigerian Correctional Serbice’ bai nuna wani canji daga yadda aka san su a daba a cikin tsarin hukunce-hukuncen shari’a na Nijeriya.

A farko an tsara zaunar da daurarru masu laifi 50,000 ne a gidajen gyaran halin amma a halin yanzu gidajen yarin kasar nan na dauke ne da masu laifi fiye da mutum 73,000.

  • An Gabatar Da Rahoton Bincike Kan Harin Da CIA Ta Kai Ga Sauran Kasashe Ta Yanar Gizo

Tabbas wannan cunkoson ya haifar da matsaloli da daman gaske wadanda suka hada da rashin tsafta, rashin samun kulawa ta magunguna ga marasa lafiya da kuma yadda ake samun karuwa cututtuka da kuma yadda daurarrau ke kara kangarewa bayan sun fito daga wadannan gidajen gyaran halin fiye da yadda suka shiga tunda farko.

Amma kuma cikin manya-manyan matsalolin da ake fuskanta su ta na yadda ake samun karuwar daurarun da ke jiran hukuncin kisa. Kwanaki Hukumar Kula da Gidajen Gyaran halin ta fitar da bayanin cewa a halin yanzu akwai fiye da mutum 3,298 da ke jiran a yanke musu hukuncin kisa a gidajen yari daban-daban a fadin kasar nan. Jami’in Watsa Labaran Hukumar, Abubakar Umar, ya bayyana cewa, ba a cika gaggauta zartar da hukuncin kisa ba da zaran an yanke ba.

Ya kara da cewa, ana daukar dogon lokaci a saboda yadda ake samun daukaka karar hukuncin da aka yanke a manyan kotuna.

Labarai Masu Nasaba

An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

“Wasu masu laifin kan yi jiran fiye da shrekara 15 kafin a yanke musu hukuncin. Suna nan suna jiran a zo a yanke musu hukuncin kisan kamar yadda kotu ta yanke. Muna na da su da dama, a yanzu a kwai mutum 3,298 da ke jiran hukuncin kisa. Su ne kusan kashi 4.5 na yawan daurarrun da muke da su a gidajen gyaran hali a fadin kasar nan,” in ji shi.
Tabbas hukuncin kisa wani abu ne da aka ci gaba da takaddama a kai, wasu na ganin alfanunsa wasu kuma na ganin bashi da wani amfani a tsarin ladaftar da rayuwar al’umma suna kuma kira da a gaggauta soke shi gaba daya.
Ra’ayin wannan jaridar a nan shi ne, duk kuwa da ra’ayin da wani yake da shi a kan hukuncin kisan, a bayyana yake cewa, bai kamata a bar daurarrau masu jiran hukuncin kisa su dauki dogon lokaci suna jiran a yanke musu hukucin ba, wannan ba a bin da za a amince da shi ba ne.
A lokutta da dama a barin dauraru masu jiran hukuncin kisa su dade na tsawon sherkaru ba tare da da sanin halin da suke ciki ba, wannan rashin adalci ne garesu da iyalansu da kuma al’umma gaba daya.
Daya daga cikin abin da ke haifar da wadannan matsalolin shi ne kin gwamnoni na sanya hannu a takardar hukuncin zartar da hukuncin kisan. Amma a yanzu wasu gwamnoni da dama suna jinkirin sanya hannu a kan takardar hukuncin kisan saboda abubuwan da suka shafi siyasa da sauransu. Wannan ya sanya dauraru da ke jiran hukuncin kisa suke ci gaba da zaman jiran dirshan ba tare da sanin yaushe za a yanke musu hukuncin ba.
Ida za a iya tunawan tun da aka dawo mulkin farar hula a shekara 1999, gwamnoni 2 ne kawai suka sanya hannu a kan zartar da hukuncin kisa ga daurarru na fadin kasar nan.
Za kuma a iya tunawa da cewa, tsohon gwamnan Jihar Kano, Ibrahim Shekarau ne na farko da ya sanya hannu a zartar da hukuncin kisa a shekarar 2006, yayin da Gwamna Adams Oshiomhole ya zama na biyu a shekarar 2012.
Tsohon gwamnan Kano ya zartar da hukuncin kisan wasu dauraru ne da ake jiran hukuncin kisa a inda aka zartar musu da hukuncin ba tare da bata lokaci ba, yayin Oshiomhole ya sa hannu a kisan mutum biyu a jiharsa ta Edo.
Yayin da za a iya amincewa da ana iya samun gwamnonin da suke adawa da hukuncin kisa amma ya kuma kamata a fahimci cewa, tuni kotu ta samu wadannna mutanen da laifukkan da ake zargin da su kuma ta yanke musu hukuncin na kisa.
A ra’ayinmu, kin sanya hannu a hukuncin kisan da gwamnoni suke kin yi kamar suna danne hukucin kotuna ke nan wanda hakan kuma yana nuna suka katsalandan ga hurumin kotunan ke nan. Wannan kuma ba adalci ne ba ga daurarun kuma yana nuna cewa, za a iya amfani da karefin siyasa wajen canza hukunce-hukuncen da kotuna suke yankewa a kasar nan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugabannin Da Aka Zaba Na Da Jan Aikin Hada Kan Nijeriya – Lawan

Next Post

‘Yan Nijeriya 376 Aka Kwaso Daga Sudan – Minista Sadiya

Related

An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya
Labarai

An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

3 hours ago
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

13 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

15 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

16 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

20 hours ago
Daurarru
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

21 hours ago
Next Post
‘Yan Nijeriya 376 Aka Kwaso Daga Sudan – Minista Sadiya

'Yan Nijeriya 376 Aka Kwaso Daga Sudan - Minista Sadiya

LABARAI MASU NASABA

Amfanin Ganyen Mangwaro Ga Masu Ciki

Amfanin Ganyen Mangwaro Ga Masu Ciki

June 8, 2025
Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

June 8, 2025
An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

June 8, 2025
Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.