• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bauchi Ta Kori Ma’aikata 2 Kan Amfani Da Takardun Bogi Don Cinye Kudin Mamaci

byKhalid Idris Doya
2 years ago
Bauchi

Hukumar Kula Da Ma’aikata ta jihar Bauchi ta sake korar wasu ma’aikatan gwamnati biyu masu suna Nasiru Samaila da Anas Jibrin bisa samunsu da laifin amfani da takardun bogi domin cinye ma wani mamacin kudadensa. 

Ma’aikatan biyu, su na aiki ne a karkashin ma’aikatar kudi ta jihar an zargesu da karkatarwa da sama da fadi da naira N332, 000 mallakin wani tsohon ma’aikatacin ma’aikatar Jibrin Adamu Zalanga (wanda ya rasu ma a halin yanzu) wanda a cewar hukumar, wannan dabi’ar ta saba wa sashin dokokin aikin gwamnati sashi na 327.

  • Wakilin Jaridar Leadership Na Kano Ya Rasu
  • Kalubalen Hada Kan ‘Ya’yan Jam’iyyar APC Da Ke Gaban Ganduje 

Hukumar ta cimma wannan matsalar korar nasu ne a yayin zamanta karo na 18 da ya gudana a ranar 15 ga watan Agustan 2023.

A sanarwar manema labarai da jami’in yada labarai na hukumar Saleh Umar ya fitar a ranar Juma’a ya ce, “A yayin zaman da hukumar ta yi kan kes din kwamitin kula da ladabtarwa, ma’aikata guda biyu wanda aka samu da laifin amfani da takardun jabu domin samun damar karkatar da kudi da yawansu ya kai N332,000 mallakin wani tsoho kuma marigayin ma’aikacin ma’aikatar kudi na jihar Bauchi (Jibrin Adamu Zalanga)”.

“Wannan matakin nasu ya saba wa sashi 327 na dokokin tsarin aikin gwamnati kuma jami’an biyu sun amsa laifukansu a yayin amsa tambayoyin da ma’aikatar ta musu,” Umar ya shaida.

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Malam Saleh Umar ya yi kuma yi bayanin cewa tun da farko ‘yansanda sun kama ma’aikatan biyu tare da gurfanar da su a gaban babban kotun majistire domin samun hukunci daidai da laifukansu.

A cewarsa a yayin zaman hukumar ta kuma amince da karin girma ga wasu jami’ai 73 bisa kwazonsu da cancantarsu, kana an yi sauyi ga wasu mutum 11.

Shugaban hukumar, Alhaji Abubakar Usman Madakin Bunun Bauchi wanda ya jagoranci zaman, ya ce, kesa-kesan badakar kudade da suke samu na matukar damunsu.

Ya gargadi ma’aikata da suke jin tsoron Allah a dukkanin ayyukansu inda ya ce duk wanda ya kuma ki ji to ba zai ki gani ba.

A fadinsa za su kara sanya ido wajen dakile irin wannan mummunar dabi’ar.

Idan za ku tuna dai a kwanakin baya hukumar ta dakatar da izinin daukan aikin Ibrahim Garba wanda ma’aikaci ne a hukumar kula da fansho ta jihar bisa kamasa da laifin cinye kudin wani mamacin dan fansho.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Next Post
Sin: Kasashen Sin Da Afirka Za Su Nuna Abin Misali Wajen Inganta Gina Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Daukacin Bil-Adama

Sin: Kasashen Sin Da Afirka Za Su Nuna Abin Misali Wajen Inganta Gina Al'umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Daukacin Bil-Adama

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version