ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bauchi Ta Kori Ma’aikata 2 Kan Amfani Da Takardun Bogi Don Cinye Kudin Mamaci

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Bauchi

Hukumar Kula Da Ma’aikata ta jihar Bauchi ta sake korar wasu ma’aikatan gwamnati biyu masu suna Nasiru Samaila da Anas Jibrin bisa samunsu da laifin amfani da takardun bogi domin cinye ma wani mamacin kudadensa. 

Ma’aikatan biyu, su na aiki ne a karkashin ma’aikatar kudi ta jihar an zargesu da karkatarwa da sama da fadi da naira N332, 000 mallakin wani tsohon ma’aikatacin ma’aikatar Jibrin Adamu Zalanga (wanda ya rasu ma a halin yanzu) wanda a cewar hukumar, wannan dabi’ar ta saba wa sashin dokokin aikin gwamnati sashi na 327.

  • Wakilin Jaridar Leadership Na Kano Ya Rasu
  • Kalubalen Hada Kan ‘Ya’yan Jam’iyyar APC Da Ke Gaban Ganduje 

Hukumar ta cimma wannan matsalar korar nasu ne a yayin zamanta karo na 18 da ya gudana a ranar 15 ga watan Agustan 2023.

ADVERTISEMENT

A sanarwar manema labarai da jami’in yada labarai na hukumar Saleh Umar ya fitar a ranar Juma’a ya ce, “A yayin zaman da hukumar ta yi kan kes din kwamitin kula da ladabtarwa, ma’aikata guda biyu wanda aka samu da laifin amfani da takardun jabu domin samun damar karkatar da kudi da yawansu ya kai N332,000 mallakin wani tsoho kuma marigayin ma’aikacin ma’aikatar kudi na jihar Bauchi (Jibrin Adamu Zalanga)”.

“Wannan matakin nasu ya saba wa sashi 327 na dokokin tsarin aikin gwamnati kuma jami’an biyu sun amsa laifukansu a yayin amsa tambayoyin da ma’aikatar ta musu,” Umar ya shaida.

LABARAI MASU NASABA

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

Malam Saleh Umar ya yi kuma yi bayanin cewa tun da farko ‘yansanda sun kama ma’aikatan biyu tare da gurfanar da su a gaban babban kotun majistire domin samun hukunci daidai da laifukansu.

A cewarsa a yayin zaman hukumar ta kuma amince da karin girma ga wasu jami’ai 73 bisa kwazonsu da cancantarsu, kana an yi sauyi ga wasu mutum 11.

Shugaban hukumar, Alhaji Abubakar Usman Madakin Bunun Bauchi wanda ya jagoranci zaman, ya ce, kesa-kesan badakar kudade da suke samu na matukar damunsu.

Ya gargadi ma’aikata da suke jin tsoron Allah a dukkanin ayyukansu inda ya ce duk wanda ya kuma ki ji to ba zai ki gani ba.

A fadinsa za su kara sanya ido wajen dakile irin wannan mummunar dabi’ar.

Idan za ku tuna dai a kwanakin baya hukumar ta dakatar da izinin daukan aikin Ibrahim Garba wanda ma’aikaci ne a hukumar kula da fansho ta jihar bisa kamasa da laifin cinye kudin wani mamacin dan fansho.

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora

MASU ALAKA

Bauchi
Labarai

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Bauchi
Labarai

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato
Manyan Labarai

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
Next Post
Sin: Kasashen Sin Da Afirka Za Su Nuna Abin Misali Wajen Inganta Gina Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Daukacin Bil-Adama

Sin: Kasashen Sin Da Afirka Za Su Nuna Abin Misali Wajen Inganta Gina Al'umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Daukacin Bil-Adama

LABARAI MASU NASABA

Bauchi

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Bauchi

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.