ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kalubalen Hada Kan ‘Ya’yan Jam’iyyar APC Da Ke Gaban Ganduje 

…Zan Sake Gyara APC –Ganduje

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Ganduje

Tsohon gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje ya zama sabon shugaban APC ne a yayin zaman kwamitin zartarwa na jam’iyyar karo na 12 da ya gudana a Abuja.

Kwamitin zantarwa ya kasance shi ne na biyu mafi girma wajen yanke hukunci a jam’iyyar APC kuma mambobinsa sun hada da shugaban kasa, mataimakin shugaban kasa, gwamnonin APC wadanda suka kasance mambobi a kwamitin gudanarwa da shugabannin jam’iyyar na jihohi da dai sauransu.

  • Gwamnatin APC Ta Kara Ingiza ‘Yan NIjeriya Cikin Bakin Talauci – PDP

An dai zabi Ganduje a matsayin shugaban jam’iyyar bayan murabis din tsohon gwamnan Jihar Nasarawa, Sanata Abdullahi Adamu wanda ya fito daga yankin arewa ta tsakiya.

ADVERTISEMENT

Ganduje ya kasance shugaban APC na shida bayan shudewar mulkin shugabanin da suka jagoranci jam’iyyar, Cif Bisi Akande daga 2013 zuwa 2014, Cif John Odigie-Oyegun daga 2014 zuwa 2018, Kwamard Adams Oshiomhole daga 2018 zuwa 2020). Mai Mala Buni daga 2020 zuwa 2022 da kuma Sanata Abdullahi Adamu daga 2022 zuwa 2023.

Wannan shi ne karon farko da wani shugaban jam’iyyar na kasa ban da mai rikon kwarya ya zama shugaban jam’iyyar bayan ganawar kwamitin zartarwa tun bayan kafa ta a shekarar 2013.

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

Idan za a tuna, wakilai ne suka zabi tsofaffin gwamnonin Jihar Edo, Oshiomhole da Odigie-Oyegun, da kuma Sanata Adamu wadanda suka kasance jiga-jigan shugabannin jam’iyyar na kasa a babban taron da jam’iyyar ta gudanar.

An zabi Odigie-Oyegun a babban taron jam’iyyar APC na kasa da aka gudanar a watan Yunin 2014, shi kuwa Oshiomhole ya zama shugaban jam’iyyar ne a taron da aka gudanar a watan Yunin 2018, yayin da Adamu ya zama shugaban jam’iyyar a babban taron kasa da aka gudanar a dandalin Eagle Skuare a watan Maris 2022.

Buni ya zama shugaban riko na jam’iyyar APC a lokacin wani taro da zartarwa ta gudanar a watan Yunin 2020, amma bai kasance zababben shugaban jam’iyyar kasa ba. An bai wa kwamitin Buni wa’adin lokacin da zai shirya babban taron kasa don zaben sabbin shugabannin APC.

Cif Akande wanda ya zama shugaban rikon kwarya a yayin taron jiga-jigan jam’iyyar a matsayin wani bangare na ka’idojin rajistar jam’iyyar kuma ya mika ragamar shugabancin jam’iyyar ga Odigie-Oyegun a lokacin da aka zabe shi a babban taron jam’iyyar a shekarar 2014.

Sai dai lamarin Ganduje ya bambanta, domin ya maye gurbin Adamu ne, wanda ya fito daga yankin arewa maso yamma a yayin taron kwamitin zartarwa ba ta hanyar zaben wakilai ba a lokacin babban taro na kasa.

Masu ruwa da tsaki sun bayyana cewa lamarin ya yi daidai da tanade-tanaden kundin tsarin mulkin jam’iyyar, wanda aka yi wa kwaskwarima a shekarar 2022.

Ita dai kwamitin zartarwa na jam’iyyar ya dagara ne da sahi na 13:3 (ii) na kundin tsarin mulkin jam’iyyar, wanda ya sa Ganduje ya zama shugaban jam’iyyar.

Amma babban abun tambayar shi ne, ko Ganduje zai iya hada kan ‘ya’yan da kuma samun goyon bayan jiga-jigan jam’iyyar APC, musamman daga shiyyar arewa ta tsakiya da sauran shiyyoyin domin ya samu nasara, ko kuma zai bi samun wadanda suka gabace shi wadanda suka bar mukamin tun kafin wa’adinsu ya kare.?

Wannan shi ne tambayoyi da masu sharhi suke yi, musamman yadda yankin arewa ta tsakiya ke ganin cewa an dakile su, inda suke cewa ya kamata yankin ya ci gaba da rike mukamin bisa la’akari da cewa wa’adin Adamu bai kare ba an tilasta masa yin murabus ne.

To sai dai kuma akwai ayar tambaya kan ko sabon shugaban jam’iyyar zai iya magance rudanin da ke cikin jam’iyyar ya mayar da ita kan tafarkinta ko kuma shi ma zai barta ta ci gaba da tafiya yadda aka saba.

Masu fashin baki sun bayyana cewa a halin yanzu dai jam’iyyar babu hadin kai saboda rikice-rikicen da ke faruwa da kuma yadda Ganduje ya samu zama shugaban jam’iyyar.

Idan za a iya tunawa dai, mashawarcin jam’iyyar kan harkokin shari’a, Ahmed El-Marzuk, ya yi murabus daga kwamitin gudanarwar jam’iyyar.

Ya yi murabus ne a wata sanarwa dauke da sa hannun mai ba shi shawara na musamman, Abdul Halim Adamu, inda ya ce ba zai iya aiki da Ganduje ba.

Duk da cewa akwai alamun ana zarginsa da rashin gaskiya da rikon amana wajen tafiyar da jam’iyyar, El-Marzuk ya yi murabus ne lokacin da Ganduje ya zama shugaban jam’iyyar.

Haka zalika, mataimakin shugaban jam’iyyar reshen arewa maso yamma, Salihu Mohammed Lukman ya yi murabus bayan ya nuna adawa da shirin maye gurbin Adamu da Ganduje, inda ya dage cewa arewa ta tsakiya ta ci gaba da rike mukaminta.

…Zan Sake Gyara APC –Ganduje

A jawabinsa na karbar ragamar shugabancin jam’iyyar, Ganduje ya ce gwamnatinsa za ta sake gyara jam’iyyar da inganta dimokuradiyyar cikin gida da hadin kai da kuma kara yawan kujerun zartarwa da na majalisar dokoki da jam’iyyar ke da su a halin yanzu.

Gwamna Ganduje ya ce shugabancinsa zai samar da jagoranci mai kyau ga dukkan ‘ya’yan jam’iyyar da ke takarar mukaman siyasa daban-daban a kasar nan. Ya jaddada cewa zabukan fid da gwani a jam’iyyar za su kasance cikin gaskiya da sahihance a karkashin kulawarsa.

Ya ce, “A karkashin kulawata, za a bi tsarin dimokuradiyyar cikin gida tare da tuntubar juna da kuma tabbatar da jam’iyyar ta yi aiki kafada da kafada da dukkan ‘ya’yanta.

“Dukkanmu mun amince cewa dole ne mu hada kan ‘ya’yan jam’iyyar domin samun goyon baya ga gwamnatinmu da kuma tabbatar da tunkarar kalubalen da ‘yan Nijeriya ke fuskanta a kullum.”

Ganduje
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Rahotonni

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF
Rahotonni

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
Next Post
Wakilin Jaridar Leadership Na Kano Ya Rasu

Wakilin Jaridar Leadership Na Kano Ya Rasu

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.