• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bayan Cinnawa Masallaci Wuta, Mutane 11 Sun Rasu A Kano

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
in Al'ajabi, Manyan Labarai
0
Bayan Cinnawa Masallaci Wuta, Mutane 11 Sun Rasu A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kawo yanzu an tabbatar da mutuwar mutane 11 bayan da wani matashi mai suna Shafi’u Abubakar ya yi kwantan ɓauna ya cinnawa wasu masallata wuta lokacin da suke tsaka da yin sallar Asuba a garin Gadan da ke ƙaramar hukumar Gazawa.

Kawo yanzu an tabbatar da mutuwar mutane 11 bayan da wani matashi mai suna Shafi’u Abubakar ya yi kwantan ɓauna ya cinnawa wasu masallata wuta lokacin da suke tsaka da yin sallar Asuba a garin Gadan da ke ƙaramar hukumar Gazawa

  • An Dakatar Da Likita Saboda Sakaci A Jihar Kano
  • Matashi Ya Banka Wa Masallaci Wuta Yayin Da Ake Sallah A Kano

Iftila’in dai ya faru ne a jiya Laraba, in da Matashin mai shekaru 38, ya ce ya yi hakan ne sakamakon fushin rikicin rabon gado, bayan ya cimma wutar ne ya kuma kulle ƙofar masallacin don kar wani ya samu damar ficewa.

An dai ruwaito cewa lokacin da lamarin ya afku akwai kimanin mutane 40 da suke sallar Asuba a cikin masallacin, bayan samun damar fitar da su ne aka garzaya asibiti domin duba lafiyarsu, sai dai kash 11 daga cikinsu sun riga mu tafiya gidan gaskiya.

Wani mazaunin garin mai suna Rabi’u Gadan ya shaidawa LEADERSHIP Hausa cewa; tuni dai har an gudanar da jana’izar 8 daga cikinsu Kuma na shirye-shiryen yinta ragowar ukun. Rabi’u ya ce harin masallacin ba wannan ne ta’addacin da matashi Shafi’u ya taɓa yi ba a ƙauyen nasu, domin ya taɓa yi wa yayanninsa biyu rutse kuma ya kai kansa wurin ƴan sanda ya ce wai ya kashe su.

Labarai Masu Nasaba

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

Wani mazaunin garin mai suna Malam Garba ya ce; Da ma can matashin fitinanne ne don har an taɓa kai shi gidan asibitin masu motsin ƙwaƙwalwa amma likita suka ce lafiyarsa ƙalau, kuma a lokacin da ya ƙalubalanci danginsa da cewa lallai sai sun ba shi rabon gadonsa, sai ku raba suka ba shi. Don haka lafiyarsa kalau ya cinna wutar, kuma biyu daga cikin waɗanda suka rasu kawunnansa ne.

Shi dai wannan matashi yanzu haka yana can tsare a hannun jami’an tsaro ana cigaba da bincike.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yansandan jihar KanoAsibitiDSSkano
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jami’ar FUBK Ta Gudanar Da Bikin Ɗaukar Sabbin Ɗalibai 2, 217 A Kebbi

Next Post

Gwamna Inuwa Ya Ƙaddamar Da Sabon Kamfanin Taki A Gombe

Related

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
Da ɗumi-ɗuminsa

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

2 hours ago
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

4 hours ago
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi
Manyan Labarai

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

8 hours ago
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
Manyan Labarai

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

9 hours ago
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
Manyan Labarai

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

23 hours ago
DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu
Da ɗumi-ɗuminsa

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

1 day ago
Next Post
Gwamna Inuwa Ya Ƙaddamar Da Sabon Kamfanin Taki A Gombe

Gwamna Inuwa Ya Ƙaddamar Da Sabon Kamfanin Taki A Gombe

LABARAI MASU NASABA

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

September 17, 2025
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

September 17, 2025
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

September 17, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

September 17, 2025
Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

September 17, 2025
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

September 17, 2025
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.