ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bayan Ficewar Ayu, PDP Ta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Fayose, Shema Da Anyim

by Sadiq
3 years ago
PDP

Shugabancin jam’iyyar PDP na kasa ya janye dakatarwar da aka yi wa tsohon gwamnan Jihar Katsina Ibrahim Shema da tsohon gwamnan Jihar Ekiti, Ayodele Fayose da Sanata Pius Anyim da Farfesa Dennis Ityavyar da Dikta Aslam Aliyu.

Har ila yau, ta janye dakatarwar da ta yi wa Gwamna Samuel Ortom na Jihar Benue na gurfana da shi a gaban kwamitin ladabtarwa bisa zargin cin zarafin jam’iyya.

  • Zaɓaɓɓen Gwamnan Kano Ya Naɗa Sakataren Yaɗa Labarunsa
  • Majalisa Ta Yi Taron Jin Ra’ayoyin Jama’a Kan Kudirin Dokar Kafa Hukumar Kula Da Almajirai

Sakataren yada labaran PDP na kasa, Debo Ologunagba, ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis bayan wani taron kwamitin zartaswa na jam’iyyar a Abuja.

ADVERTISEMENT

Ya kuma bayyana cewa jam’iyyar a shirye take don ganin an sasanta tsakanin mambobinta.

Ya ce, “Kwamitin zartaswa na kasa na jam’iyyar PDP a taronta na yau, Alhamis, 30 ga watan Maris, 2023 ya tattauna sosai kan abubuwan da suka faru a jam’iyyar.

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

“Kwamitin ya amince da yin sulhu tsakanin shugabannin jam’iyya da masu ruwa da tsaki don samar da jam’iyya mai hadin kai don ci moriyar mambobinmu da ‘yan Nijeriya baki daya.

“Sakamakon abin da ya faru shi ne an sauya matakin da Gwamnan Jihar Benue, Samuel Ortom ya yi wa kwamitin ladabtarwa na kasa.

“Kwamitin a cikin wannan yanayin ta sauya dakatarwar da aka yi wa mambobin babbar jam’iyyarmu.

“Dole ne jam’iyyar PDP ta mai da hankali yayin da muke ci gaba da daukar dukkan matakan da suka dace na kwato hakki dan takarar shugaban kasa, Atiku Abubakar, da aka kwace a ranar Asabar 25 ga Fabrairu, 2023, a kotun sauraren kararrakin zaben shugaban kasa.”

Idan za a tuna cewa jam’iyyar PDP ta dakatar da shugabannin jam’iyyar biyar a karkashin jagorancin shuganacin Iyorchia Ayu.

Sai dai sabon shugaban rikon kwarya na jam’iyyar PDP, Aliyu Madagum ya jagoranci yin sulhu a tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7
Da ɗumi-ɗuminsa

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

November 15, 2025
Yanzu Satar Da Kuka Yi Ba Ta Da Amfani: Kwankwaso Ga Gwamnonin APC
Manyan Labarai

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

November 15, 2025
NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama
Manyan Labarai

NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama

November 15, 2025
Next Post
Dan Siyasar Zambia: “Taron Kolin Diplomasiya” Ba Zai Canja “Makircin Diplomasiyar Amurka” Ba

Dan Siyasar Zambia: “Taron Kolin Diplomasiya” Ba Zai Canja “Makircin Diplomasiyar Amurka” Ba

LABARAI MASU NASABA

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

November 15, 2025
Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

November 15, 2025
Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

November 15, 2025
Za A Yi Gwanjon Rigunan Messi Na Gasar Kofin Duniya Ta 2022 Da Kudi Tsagwagwa

Ina Son Kasancewa Cikin Koshin Lafiya Kafin Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Messi

November 15, 2025
Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

November 15, 2025
Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

November 15, 2025
Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

November 15, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

November 15, 2025
An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

November 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.