ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bayan Ficewar Ayu, PDP Ta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Fayose, Shema Da Anyim

by Sadiq
3 years ago
PDP

Shugabancin jam’iyyar PDP na kasa ya janye dakatarwar da aka yi wa tsohon gwamnan Jihar Katsina Ibrahim Shema da tsohon gwamnan Jihar Ekiti, Ayodele Fayose da Sanata Pius Anyim da Farfesa Dennis Ityavyar da Dikta Aslam Aliyu.

Har ila yau, ta janye dakatarwar da ta yi wa Gwamna Samuel Ortom na Jihar Benue na gurfana da shi a gaban kwamitin ladabtarwa bisa zargin cin zarafin jam’iyya.

  • Zaɓaɓɓen Gwamnan Kano Ya Naɗa Sakataren Yaɗa Labarunsa
  • Majalisa Ta Yi Taron Jin Ra’ayoyin Jama’a Kan Kudirin Dokar Kafa Hukumar Kula Da Almajirai

Sakataren yada labaran PDP na kasa, Debo Ologunagba, ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis bayan wani taron kwamitin zartaswa na jam’iyyar a Abuja.

ADVERTISEMENT

Ya kuma bayyana cewa jam’iyyar a shirye take don ganin an sasanta tsakanin mambobinta.

Ya ce, “Kwamitin zartaswa na kasa na jam’iyyar PDP a taronta na yau, Alhamis, 30 ga watan Maris, 2023 ya tattauna sosai kan abubuwan da suka faru a jam’iyyar.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

“Kwamitin ya amince da yin sulhu tsakanin shugabannin jam’iyya da masu ruwa da tsaki don samar da jam’iyya mai hadin kai don ci moriyar mambobinmu da ‘yan Nijeriya baki daya.

“Sakamakon abin da ya faru shi ne an sauya matakin da Gwamnan Jihar Benue, Samuel Ortom ya yi wa kwamitin ladabtarwa na kasa.

“Kwamitin a cikin wannan yanayin ta sauya dakatarwar da aka yi wa mambobin babbar jam’iyyarmu.

“Dole ne jam’iyyar PDP ta mai da hankali yayin da muke ci gaba da daukar dukkan matakan da suka dace na kwato hakki dan takarar shugaban kasa, Atiku Abubakar, da aka kwace a ranar Asabar 25 ga Fabrairu, 2023, a kotun sauraren kararrakin zaben shugaban kasa.”

Idan za a tuna cewa jam’iyyar PDP ta dakatar da shugabannin jam’iyyar biyar a karkashin jagorancin shuganacin Iyorchia Ayu.

Sai dai sabon shugaban rikon kwarya na jam’iyyar PDP, Aliyu Madagum ya jagoranci yin sulhu a tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar.

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
Dan Siyasar Zambia: “Taron Kolin Diplomasiya” Ba Zai Canja “Makircin Diplomasiyar Amurka” Ba

Dan Siyasar Zambia: “Taron Kolin Diplomasiya” Ba Zai Canja “Makircin Diplomasiyar Amurka” Ba

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.