ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bayan Ficewar Ayu, PDP Ta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Fayose, Shema Da Anyim

by Sadiq
3 years ago
PDP

Shugabancin jam’iyyar PDP na kasa ya janye dakatarwar da aka yi wa tsohon gwamnan Jihar Katsina Ibrahim Shema da tsohon gwamnan Jihar Ekiti, Ayodele Fayose da Sanata Pius Anyim da Farfesa Dennis Ityavyar da Dikta Aslam Aliyu.

Har ila yau, ta janye dakatarwar da ta yi wa Gwamna Samuel Ortom na Jihar Benue na gurfana da shi a gaban kwamitin ladabtarwa bisa zargin cin zarafin jam’iyya.

  • Zaɓaɓɓen Gwamnan Kano Ya Naɗa Sakataren Yaɗa Labarunsa
  • Majalisa Ta Yi Taron Jin Ra’ayoyin Jama’a Kan Kudirin Dokar Kafa Hukumar Kula Da Almajirai

Sakataren yada labaran PDP na kasa, Debo Ologunagba, ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis bayan wani taron kwamitin zartaswa na jam’iyyar a Abuja.

ADVERTISEMENT

Ya kuma bayyana cewa jam’iyyar a shirye take don ganin an sasanta tsakanin mambobinta.

Ya ce, “Kwamitin zartaswa na kasa na jam’iyyar PDP a taronta na yau, Alhamis, 30 ga watan Maris, 2023 ya tattauna sosai kan abubuwan da suka faru a jam’iyyar.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

“Kwamitin ya amince da yin sulhu tsakanin shugabannin jam’iyya da masu ruwa da tsaki don samar da jam’iyya mai hadin kai don ci moriyar mambobinmu da ‘yan Nijeriya baki daya.

“Sakamakon abin da ya faru shi ne an sauya matakin da Gwamnan Jihar Benue, Samuel Ortom ya yi wa kwamitin ladabtarwa na kasa.

“Kwamitin a cikin wannan yanayin ta sauya dakatarwar da aka yi wa mambobin babbar jam’iyyarmu.

“Dole ne jam’iyyar PDP ta mai da hankali yayin da muke ci gaba da daukar dukkan matakan da suka dace na kwato hakki dan takarar shugaban kasa, Atiku Abubakar, da aka kwace a ranar Asabar 25 ga Fabrairu, 2023, a kotun sauraren kararrakin zaben shugaban kasa.”

Idan za a tuna cewa jam’iyyar PDP ta dakatar da shugabannin jam’iyyar biyar a karkashin jagorancin shuganacin Iyorchia Ayu.

Sai dai sabon shugaban rikon kwarya na jam’iyyar PDP, Aliyu Madagum ya jagoranci yin sulhu a tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar.

MASU ALAKA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Next Post
Dan Siyasar Zambia: “Taron Kolin Diplomasiya” Ba Zai Canja “Makircin Diplomasiyar Amurka” Ba

Dan Siyasar Zambia: “Taron Kolin Diplomasiya” Ba Zai Canja “Makircin Diplomasiyar Amurka” Ba

LABARAI MASU NASABA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.