ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bayan Ficewar Ayu, PDP Ta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Fayose, Shema Da Anyim

by Sadiq
3 years ago
PDP

Shugabancin jam’iyyar PDP na kasa ya janye dakatarwar da aka yi wa tsohon gwamnan Jihar Katsina Ibrahim Shema da tsohon gwamnan Jihar Ekiti, Ayodele Fayose da Sanata Pius Anyim da Farfesa Dennis Ityavyar da Dikta Aslam Aliyu.

Har ila yau, ta janye dakatarwar da ta yi wa Gwamna Samuel Ortom na Jihar Benue na gurfana da shi a gaban kwamitin ladabtarwa bisa zargin cin zarafin jam’iyya.

  • Zaɓaɓɓen Gwamnan Kano Ya Naɗa Sakataren Yaɗa Labarunsa
  • Majalisa Ta Yi Taron Jin Ra’ayoyin Jama’a Kan Kudirin Dokar Kafa Hukumar Kula Da Almajirai

Sakataren yada labaran PDP na kasa, Debo Ologunagba, ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis bayan wani taron kwamitin zartaswa na jam’iyyar a Abuja.

ADVERTISEMENT

Ya kuma bayyana cewa jam’iyyar a shirye take don ganin an sasanta tsakanin mambobinta.

Ya ce, “Kwamitin zartaswa na kasa na jam’iyyar PDP a taronta na yau, Alhamis, 30 ga watan Maris, 2023 ya tattauna sosai kan abubuwan da suka faru a jam’iyyar.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

“Kwamitin ya amince da yin sulhu tsakanin shugabannin jam’iyya da masu ruwa da tsaki don samar da jam’iyya mai hadin kai don ci moriyar mambobinmu da ‘yan Nijeriya baki daya.

“Sakamakon abin da ya faru shi ne an sauya matakin da Gwamnan Jihar Benue, Samuel Ortom ya yi wa kwamitin ladabtarwa na kasa.

“Kwamitin a cikin wannan yanayin ta sauya dakatarwar da aka yi wa mambobin babbar jam’iyyarmu.

“Dole ne jam’iyyar PDP ta mai da hankali yayin da muke ci gaba da daukar dukkan matakan da suka dace na kwato hakki dan takarar shugaban kasa, Atiku Abubakar, da aka kwace a ranar Asabar 25 ga Fabrairu, 2023, a kotun sauraren kararrakin zaben shugaban kasa.”

Idan za a tuna cewa jam’iyyar PDP ta dakatar da shugabannin jam’iyyar biyar a karkashin jagorancin shuganacin Iyorchia Ayu.

Sai dai sabon shugaban rikon kwarya na jam’iyyar PDP, Aliyu Madagum ya jagoranci yin sulhu a tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar.

MASU ALAKA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Next Post
Dan Siyasar Zambia: “Taron Kolin Diplomasiya” Ba Zai Canja “Makircin Diplomasiyar Amurka” Ba

Dan Siyasar Zambia: “Taron Kolin Diplomasiya” Ba Zai Canja “Makircin Diplomasiyar Amurka” Ba

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.