• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bayan Kwashe Shekaru A Garkame, Zulum Ya Sake Bude Kasuwar Shanu Ta Gamboru

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Bayan

Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, a ranar Asabar ya sake bude babbar kasuwar Shanu ta kasa da kasa ta Gamboru wanda aka rufe sama da shekaru bakwai sakamakon hare-haren ‘yan ta’addan Boko Haram a jihar.

Babbar kasuwar wacce take da matsuguni a Gamboru, waje ne da ake gudanar da harkokin kasuwanci sosai a iyakar karamar hukumar Ngala da ke cikin tsakiyar jihar Borno.

  • Zulum Ya Bai Wa Matasan Biu 1,000 Tallafin Miliyan 100 Don Yin Jari
  • Zulum Ya Shigar Da Marayu 7000 Makaranta A i

Gamboru ta hada iyaka da Jamhuryar Kamaru kuma hanyarta na iya hadawa zuwa N’Djamena babban birnin jamhuriyyar Chad.

Zulum wanda ya kasance a karamar hukumar ta Ngala na tsawon kwanaki biyu domin gudanar da harkokin da suka shafi jin kai, ya sake bude kasuwar ne da rakiyar babban jami’in da ke bada umarni (CO) na bataliyar soji ta 3, Lt. Col. Tolu Adedokun, tare da shugaban karamar hukumar Hon. Mala Tijjani.

Zulum ya jinjina da irin kokarin shugaban kasa Muhammadu Buhari, da rundunar sojin kasa, ‘yan sanda, hukumar tsaron farin kaya, da sauran bangarorin tsaro ciki har da na masu sa-kai da suka bada tasu gudunmawar wajen tabbatar da dawo da tsaro da zaman lafiya a jihar Borno, wanda hakan ne ya kai ga samun nasarar sake bude kasuwar.

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

Daga nan sai ya yi gargadin cewa, duk wani ko wasu dillalan shanu da aka sake kamawa da shiga cikin harkokin ta’addanci, lallai hukuma za ta dandana masa kudarsa.

Kwamishinan matasa, wasanni da yaki da fatara na jihar, Saina Buba, wanda ya jagoranci kwamitin kula da harkokin shanu a jihar, ya yi bayanin cewa a kalla duk rana ana jigilar shanu sama da 500 ko 800 zuwa kasashen makwafta daga wannan kasuwar.

A cewarsa, dubban mutane ke amfana da kasuwar ta hanyar samar musu da ayyukan yi, da kuma bunkasa harkokin kasuwanci.

Shugaban kungiyar ‘yan kasuwar shanu ta jihar, Alhaji Yakuba Goni, ya gode wa gwamnan bisa sake bude kasuwar tare da shan alwashin cewa za su taimaka wajen kyautata lamura.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 
Manyan Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati
Labarai

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da KuÉ—aÉ—en TETFund Da Ba Su Kashe Ba
Labarai

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da KuÉ—aÉ—en TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Next Post
Gwamnan Bauchi Ya Mika Wa Sarkin Katagum Sandar Girma

Gwamnan Bauchi Ya Mika Wa Sarkin Katagum Sandar Girma

LABARAI MASU NASABA

An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

October 9, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

October 9, 2025
SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da KuÉ—aÉ—en TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da KuÉ—aÉ—en TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.