ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bayan Kwashe Shekaru A Garkame, Zulum Ya Sake Bude Kasuwar Shanu Ta Gamboru

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Bayan

Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, a ranar Asabar ya sake bude babbar kasuwar Shanu ta kasa da kasa ta Gamboru wanda aka rufe sama da shekaru bakwai sakamakon hare-haren ‘yan ta’addan Boko Haram a jihar.

Babbar kasuwar wacce take da matsuguni a Gamboru, waje ne da ake gudanar da harkokin kasuwanci sosai a iyakar karamar hukumar Ngala da ke cikin tsakiyar jihar Borno.

  • Zulum Ya Bai Wa Matasan Biu 1,000 Tallafin Miliyan 100 Don Yin Jari
  • Zulum Ya Shigar Da Marayu 7000 Makaranta A i

Gamboru ta hada iyaka da Jamhuryar Kamaru kuma hanyarta na iya hadawa zuwa N’Djamena babban birnin jamhuriyyar Chad.

ADVERTISEMENT

Zulum wanda ya kasance a karamar hukumar ta Ngala na tsawon kwanaki biyu domin gudanar da harkokin da suka shafi jin kai, ya sake bude kasuwar ne da rakiyar babban jami’in da ke bada umarni (CO) na bataliyar soji ta 3, Lt. Col. Tolu Adedokun, tare da shugaban karamar hukumar Hon. Mala Tijjani.

Zulum ya jinjina da irin kokarin shugaban kasa Muhammadu Buhari, da rundunar sojin kasa, ‘yan sanda, hukumar tsaron farin kaya, da sauran bangarorin tsaro ciki har da na masu sa-kai da suka bada tasu gudunmawar wajen tabbatar da dawo da tsaro da zaman lafiya a jihar Borno, wanda hakan ne ya kai ga samun nasarar sake bude kasuwar.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Daga nan sai ya yi gargadin cewa, duk wani ko wasu dillalan shanu da aka sake kamawa da shiga cikin harkokin ta’addanci, lallai hukuma za ta dandana masa kudarsa.

Kwamishinan matasa, wasanni da yaki da fatara na jihar, Saina Buba, wanda ya jagoranci kwamitin kula da harkokin shanu a jihar, ya yi bayanin cewa a kalla duk rana ana jigilar shanu sama da 500 ko 800 zuwa kasashen makwafta daga wannan kasuwar.

A cewarsa, dubban mutane ke amfana da kasuwar ta hanyar samar musu da ayyukan yi, da kuma bunkasa harkokin kasuwanci.

Shugaban kungiyar ‘yan kasuwar shanu ta jihar, Alhaji Yakuba Goni, ya gode wa gwamnan bisa sake bude kasuwar tare da shan alwashin cewa za su taimaka wajen kyautata lamura.

Bayan
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ‘Yansanda Sun Cafke Tsoho Mai Shekara 70 Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 8 Fyaɗe A Bauchi

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Next Post
Gwamnan Bauchi Ya Mika Wa Sarkin Katagum Sandar Girma

Gwamnan Bauchi Ya Mika Wa Sarkin Katagum Sandar Girma

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.