• English
  • Business News
Sunday, August 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bayan Nasara A Kotun Ƙoli, Tinubu Zai Ci Gaba Da Aikin Gina Nagartacciyar Ƙasa – Minista

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Bayan Nasara A Kotun Ƙoli, Tinubu Zai Ci Gaba Da Aikin Gina Nagartacciyar Ƙasa – Minista
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan yaɗa labarai da wayar da kai, Alhaji Muhammad Idris ya bayyana cewa nasarar da Shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya samu a kotun ƙoli za ta ƙara masa himma wajen ci gaba da gudanar da ayyukan gina nagartacciyar ƙasa. 

Ministan ya bayyana haka ne a wani taron manema labarai da ya gabatar dangane da hukuncin da kotun ta yanke.

  • Tsohon Firaministan kasar Sin Li Keqiang Ya Rasu
  • Tsarin Canji Na Bai-daya Hanya Ce Ta Tsaftace Kasuwar Shinku

Tun farko, Ministan cewa ya yi maraba da bakin da suka halarci taron, wanda ya ce, an shirya ne bayan hukuncin shari’ar da Kotun Ƙoli ta yanke na tabbatar da Nasarar Tinubu. Hakan ya kawo ƙarshen ƙorafe-ƙorafen ƙararrakin da aka riƙa shigarwa a kotuna game da nasarar Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Ya ƙara da cewa “maganar shari’ar zaɓen Shugaban Ƙasa ta kare, yanzu lokaci ne da za mu tunkari aikin tafiyar da gwamnati ba tare da wani abu ya ɗauke mana hankali ba.

“Tabbas wannan babban ƙalubale ne, musamman a wannan lokaci da tattalin arziki ke fuskantar mawuyacin hali, ba a Nijeriya kaɗai ba, har duniya baki ɗaya.

Labarai Masu Nasaba

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

“Saboda haka, tilas a taru mu haɗa hannu wuri ɗaya, domin magance wannan ƙalubale da ke tunkarar mu. Shugaba Tinubu ya bayyana a fili cewa shi Shugaban Ƙasa ne na kowane ɗan Nijeriya, ba tare da bambancin yanki, ƙabila, siyasa ko addini ba.”

Minista Idris ya ce, tun bayan hawansa mulki a ranar 29 ga Mayu, Shugaba Tinubu ya na ta aiki tuƙuru wajen ƙoƙarin samun nasarar Ajandar Farfaɗo da Nijeriya, wadda ta na daga cikin dalilan sa na kishin zama shugaban ƙasa.

Ya aiwatar da manyan tsare-tsare, duk da tsaurin da tsarin ya fuskanta amma tsaurin na wani taƙaitaccen lokaci ne. Kuma ta haka ne aka gina tubalin girka ƙasaitaccen tattalin arziki, samar da yalwar da kowane ɗan Nijeriya ya cancanci ya samu.

Game da cire tallafin man fetur, Ministan cewa ya yi “Kamar yadda ku ka sani, cire tallafin fetur abu ne da ya samo tushe daga Dokar Fetur ta 2021, wadda yanzu ta ke ƙara tanadar wa Gwamnatin Tarayya da Jihohi maƙudan kuɗaɗen da za su riƙa yin ayyukan inganta rayuwa da bunƙasa ƙasa.”

Game da halin ƙunci da ake ciki a ƙasar nan, Minista Idris ya ce “Babu gwamnatin da ta san abin da ta ke yi da za ta jefa al’ummar ta cikin halin ƙunci da gangan. Shi ya sa mu ke jaddada cewa wannan hali da ake ciki zai wuce cikin taƙaitaccen lokaci nan gaba. Daga nan sai mu shiga yanayin yalwa mai dorewa.”

Ya kuma ce, Gwamnatin Tinubu na ɗaukar dukkan matakan da su ka wajaba domin sauƙaƙe wa talakawa raɗaɗin tsadar rayuwar da su ke fama da ita a yanzu.

Ya bayyana cewa, “Daga cikin hanyoyin akwai: Ƙarin Naira 35,000 kan albashin ma’aikata, har tsawon watanni shida a jere. Kafa Asusun Gina Ayyukan Raya Ƙasa na Jihohi. Ƙaddamar da sayen motoci masu aiki da gas, domin sauƙaƙa tsadar zirga-zirgar motoci.”

Idris ya bayyana cewa “nan da 2024 za a fara shirin bai wa ɗalibai rance.”

Ya ce ana kan aikin tsare-tsaren Kasafin Kuɗi na 2024. “Saboda haka ‘yan Nijeriya su kwantar da hankalin su. Wannan kasafin kuɗin na farko na Gwamnatin Tinubu zai kasance na farko wanda kacokam ya maida hankali kan samar da bunƙasar tattalin arziki da samun yalwa ga kowa da kowa.

Ya ƙara da cewa “Ina ƙara yin kira ga ‘yan Nijeriya da mu ci gaba da haƙuri, ƙasar nan za ta warware, ta bunƙasa ba da daɗewa ba. Mu na fatan samun ƙasaitacciyar ƙasar da kowa zai amfana da cin moriyar bunƙasar ta.”

A ƙarshe, Ministan ya kara nananta ikirarin Tinubu bayan da kotun koli ta tabbatar da Nasararsa, “Ajandar Farfaɗo da Nijeriya zuwa ƙasaitacciyar ƙasa ta ƙara samun karsashi. Zan ci gaba da yin aiki ba dare ba rana domin gina ƙasar da ta cancanci nagartattun mutane irin ɗaukacin mu baki ɗaya ke fatan samu.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ministan yada labaraiTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Fashin Daji Na Cin Karensu Ba Babbaka A Jihar Katsina

Next Post

Kwankwaso Ya Kaddamar Da Cibiyar Nazarin Harkokin Alkur’ani

Related

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto
Labarai

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

5 hours ago
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto
Labarai

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

8 hours ago
Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto
Labarai

Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

8 hours ago
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 
Da ɗumi-ɗuminsa

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

10 hours ago
Gwamna Fintiri Ya Karrama Kocin Super Falcons, Madugu Da Naira Miliyan 50
Labarai

Gwamna Fintiri Ya Karrama Kocin Super Falcons, Madugu Da Naira Miliyan 50

11 hours ago
Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO
Manyan Labarai

Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

11 hours ago
Next Post
Kwankwaso Ya Kaddamar Da Cibiyar Nazarin Harkokin Alkur’ani

Kwankwaso Ya Kaddamar Da Cibiyar Nazarin Harkokin Alkur'ani

LABARAI MASU NASABA

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

August 2, 2025
Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?

Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?

August 2, 2025
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

August 2, 2025
Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

August 2, 2025
Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

August 2, 2025
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

August 2, 2025
Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

August 2, 2025
Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

August 2, 2025
An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

August 2, 2025
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

August 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.