ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsarin Canji Na Bai-daya Hanya Ce Ta Tsaftace Kasuwar Shinku

by Abubakar Abba
3 years ago
Canji

Kafin daukar mataki a kan tsarin da gwamnatin tarayya mai ci ta yi na kikiro da yin amfani da kudin musayar kudaden waje a cikin kasar nan, da kasuwar musayar kudi ta kasar, ta shiga cikin halin ni ‘yasu.

Gwamnatin na da hanyoyin musayar kudade daban-daban, inda kuma a gefe daya, kamfanin jirgen sama suna da na su daban, haka suma kananan masana’antu da masana’antu na da nasu na daban da ake kira da zuba hannun jari da kuma fitar da kaya zuwa ketare wato (I&E), wanda hakan ya baiwa daidaikun mutane damar samun kudaden musayar kuadade na waje a bisa bukatarsu ta samun kudaden na musayar.

Abu mafi muni shi ne, masu bukatar samun kudaden ba sa iya samu saboda iyakance adadin da aka yi na samun kudaden na musayar.

ADVERTISEMENT

Kazakika, wadanda ke da kudaden na musayar don su sayar da su, ba a ba su damar yin hada-hadar yin kasuwancin su a bisa ko nawa suke bukatar kan farashin da suke bukatar sayar da kudaden na musayar ba.

A baya, kudaden na musayar sun dakile masu son zuba hannun jair na keatare da na cikin gida zuba hannun jarinsu domin bunkasa tattalin arzikin Nijeriya, haka kuma akwai rashin tabbas a kan kudaden na musayar, wanda hakan ya haifar da wani babban shinge ga yin hada-hadar kasuwanci.

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

Bugu da kari, masu son shigowa cikin kasar don zuba hannun jari, sai suka gwammace kodai su tsaya a gefe, ku kuma su zuba hannun jarin nasu a wasu sauran kasuwannin.

Wato ma’ana, wadanda ke son samun kudaden musayar don yin wasu ayyuka, suna samun jinkiri wajen samun kudaden wanda hakan ke sanya su dakatar da bukatarsu, ta ci gaba da neman kudaden na musayar.

Hakan ya janyo tsadar da gwamnatin kasar ke samu ta kai kimanin dala miliyan 329 a duk wata a kan tallafin na kudaden musayar.

Hakan ya nuna sanar da irin illar da ake samu a kan farashin na bai daya tun daga kan masu zuba jari daga ketare da kuma masu zuba jari na cikin gida.

Sai dai, a kulla yarjejeniya a kan kayan cikin gida, hakan ya habaka kwarin guiwar masu son zuba jari a cikin Nijeriya, akwai kuma fatan da ake da shi na kara samun bunkasar zuba hannun jari a cikin tattalin arzikin kasar.

Abu mafi sauki da ake bukata shi ne yin cinikaiyyar kudaden musayar a kan farashi daya wanda hakan zai baiwa dilolin da ke yin hada-hadar kudaden na musayar yin hada-hadar ba tare da fuskantar wani shinge ba.

Bugu da kari, a bisa rahoton da bankunan hada-hadar kasuwanci na kasar suka fitar, ya nuna cewa, a cikin ‘yan watanni uku da aka gabatar da tsarin na bai daya na hada-hadar kudaden na musayar, an ruwaito cewa, bankunan kasuwanci a cikin kasar nan, a farkon zango na shekarar 2023, sun samu dimbin riba ta musayar kudaden da aka kiyasa ta kai ta Naira Tiriliyan 1.7.

Samun wannan ribar a kan kudaden musayar kudaden, an danganta hakan ne a kan karyewar farashin Naira wadda ta kai matsayin Naira 769.25 a kan dala 1 a watan Yunin 2023, inda aka kwatanta da yadda matsayin Naira yake a  2022, inda ta rufe a kan farashin Naira 461.50 , inda ya kai a kan dala 1.

Bugu da kari, kwararru a fannin hada-hadar musayar kudi, na da yakinin cewa,  wannan sabon tsarin da gwamnatin mai ci ta kirkiro da shi, musamman domin a tabatar da an yi  tsafatattaciyar hada-hadar musayar kudade, wanda tuni wannan tsarin a dai-daikun mutane da kuma ‘yan kasuwa  suka fara ganin fa’idarsa, zai bayar da gagarumar gudunmawa wajen farfado da tattalin arzikin kasar nan .

Biyo bayan daidaita farashin kudin muyasar, masu abokan huddar da ke ajiye kudade a bankuna, wato (DMBs), suma sun yi saurin rungumar tsare-tsaren da bankunna kasuwanci suka kirkiro, musamman bisa nufin samar da sauki a wajen yin musayar kudi.

Bugu da kari, a bisa zabin sauya kudaden musaya zuwa takardar Naira, ta hanyar yanar Gizo, wannan a yanzu, ya baiwa masu huddda da bankuna damar cire kudi a bankuna ba tare da wata matsala ba haka ba  sun je kasuwar bayan fage don yin musayar kudi ba.

Wannan sauyin ya kara kwarin gwuiwa a wajen daidaita tsarin farashin na kudin musaya kari da jajircewar gwamnatin tarayya na tabbatar da ana bin diddigi da kuma gudanar da sahihiyar kasuwar ta musayar kudi.

Kazalika, tsarin ya kara baiwa bankunan kwarin guiwa wajen kirkiro da abubuwa da kuma gabatar da lalubo da mafita a kan yadda za su yi hada-hada da abokan huddarsu.

Babban misali daya shi ne, yadda tsarin ya bayar da dama sake farfado da asusun masu ajiya na bankuna da aka dakarar da su daga yin aiki, saboda masu amfani da asusun sun daina yin amfani da su, wanda kuma tsarin yaba su damar samun rance kudi da suka kai har zuwa kashi 85 a cikin dari.

Dakatar da yin amfani da Kati na hada-hadar yin hadar-hadar Niara na kasa da kasa, wannan ya baiwa bakunan damar baiwa daidaikun mutane damar yin kasuwanci daga kasa zuwa wata kasa, wanda hakan ya dakile kalubalen da ake fuskanta a hada-hadar kudaden kasa da kasa

Sanarwar dokokin hakan ya kara farashin yarjejeniyar kudin Yuro na kasar nan, inda wasu suka kara yawan farashi a cikin watanni.

Hakazalika,  bayar da damar a 2033  ta karu daga kashi 2.4  zuwa kashi  78.625, wanda hakan ya zama shi ne babban karin da aka samu a cikin sama da wata biyar.

A cewar Babban Jami’a a Bolition Cap, Subomi Plumptre, kasauwar hada-hadar kudaden musayar kudin za a kara samun matukar yin gasa, musamman ganin cewa, baokan hudda za su yi sauya dala kai tsaye, ta hanyar hada-hadar yanar Gizo

Ta ce, wannna zai kara bayar da kwarin guiwa wajen samar da kirkiro da dabaru wanda kuma hakan zai bayar da dama wajen rage hada-hadar farashin kudaden musaya ga alummar gari.

Shi kuwa Baban Jami’i a Cibiyar daukaka kasuwanci mai zaman kanta wato (CPPE), Dakta Muda Yusuf, a cikin wata sanarwa da ya fitar a kwanan baya ya bayyana cewa, daga darajar ta muysar kudi, zai bayar da dama wajen zuba hannun jari da samar da ayyukan yi da zagayar kudade, inda kuma za ta kara wa masu son zuba jari kwarin guiwa.

Kazalika ya bayyana cewa, hakan zai rage cin hanci da rasahwa da dakile aikata sauran badakala da sauransu.

Bugu da kari, shi ma wani masani a fannin tattalin azrki Kelbin Emmanuel ya sanar da cewa, wannan matakin zai zai kara samar da kudaden shiga ga kamfanonin gwamnati a bisa farashin masu zuba jari da kuma masu fitar da kaya zuwa ketare.

Ya kuma yi amanna da cewa, wadanan sauye-sauyen, za su kara bunkasa tattalin arzikin kasar nan.

Sai dai, ya bayyana cewa, sauye-sauyen za su iya zuwa da kalubale, inda ya buga misalai da samun karuwar hauhawan farashin kaya da gudanar da ayyuka

Ugwu, mai fashin baki ne a kan hada-hadar kudi da ke da zama a Abuja.

Canji
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Rahotonni

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF
Rahotonni

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
Next Post
Abinda Ya Kamata Ku Sani Akan Wasan El Classico

Abinda Ya Kamata Ku Sani Akan Wasan El Classico

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.