• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bikin Al’adun Gargajiya Na Rigata Karo na 3 Zai Gudana A 8 Ga Fabrairu A Yauri

by Umar Faruk
1 year ago
in Labarai
0
Bikin Al’adun Gargajiya Na Rigata Karo na 3 Zai Gudana A 8 Ga Fabrairu A Yauri
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shahararren Bikin Rigata da Al’adu na Yauri zai gudana ne daga ranar 8 zuwa 10 ga Fabrairu, 2024 a tsohon birnin Yelwa-Yauri a Jihar Kebbi.

Shugaban bikin na kasa wanda shine sakataren gwamnatin jiha Alhaji Yakubu Bala Tafidan Yauri ne ya bayyana hakan a wata ganawa da manema labarai a Birnin Kebbi.

  • Gwamna Nasir Ya Amince Da Fitar Da Naira Miliyan 27.5 Don  Biyan Kuɗin Ɗaliban Lauyoyi Na Jihar Kebbi
  • Auren Gata : Gwamnatin Jihar Kebbi Ta Aurar Da Mata 300

Taron zai gabatar da kaddamar da littafi kan tarihin Yauri daga 1411 zuwa yau, baje kolin kasuwanci, baje kolin amfamin gona, wasan kwaikwayo na al’adu da babban wasan karshe na Rigata.

Mai martaba Sarkin Yauri na 42, Dr. Muhammad Zayyanu Abdullahi ne ya dauki nauyin sake farfado da bikin na Rigata da gwamnatin jihar Kebbi ta dauki nauyinta a matsayin babban taron al’adun.

Rigata kalma ce a yaren yankin Gungawa da ke nuna yakin ruwa.

Labarai Masu Nasaba

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Bikin ya kunshi motsa jikin koguna da suka hada da wasannin ruwa da kuma nishadantarwa wanda aka fara shekaru 200 da suka gabata a matsayin nunin karfin sojojin ruwa na ‘yan bindigar Gungu inda mayakan na Gungu suka kai hari a kan kogin Niger mai hatsarin gaske.

Sai dai mayaƙan sun kasance suna hawa kwale-kwale masu girma dabam da makamai daban-daban domin kai farmaki kan mamayabin da ke cikin ruwa.

Har ila yau, motsin ruwa ya kasance a matsayin atisayen horar da mayaka na Gungu masu zuwa.
Zuwan Turawa ya sa gwamnatin mulkin mallaka ta hana farautar kadodin ruwa don kiyaye irin wannan nau’in.

Bayan haka, Rigata ta zama babban baje kolin arziki, iko da tasiri yayin bukukuwan aure na manyan gidaje.

Lamarin ya ci gaba har zuwa ziyarar da Marigayi Firimiyan Arewacin Nijeriya Sir Ahmadu Bello Sardaunan Sokoto ya kai Yelwa-Yauri inda aka shirya Rigata tare da nuna amfani gona domin karrama Firimiya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Arewacin NijeriyaBikin Al'aduRuwan Neja
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kamfanonin Ketare Dake Kasar Sin Sun Amince Da Makomar Tattalin Arzikinta

Next Post

An Gudanar Da Bikin Aza Harsashin Ginin Rumfar Kasar Sin A Bikin Baje Kolin Hajoji Na Duniya Na Osaka Kansai Na Japan

Related

UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

5 hours ago
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista
Labarai

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

6 hours ago
gaza
Labarai

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

7 hours ago
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa
Labarai

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

9 hours ago
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja
Labarai

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

10 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

11 hours ago
Next Post
An Gudanar Da Bikin Aza Harsashin Ginin Rumfar Kasar Sin A Bikin Baje Kolin Hajoji Na Duniya Na Osaka Kansai Na Japan

An Gudanar Da Bikin Aza Harsashin Ginin Rumfar Kasar Sin A Bikin Baje Kolin Hajoji Na Duniya Na Osaka Kansai Na Japan

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.