• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bikin Baje Kolin CIIE: Kasashen Afirka Kar Ku Yarda A Bar Ku A Baya

by Abdulrazaq Yahuza
2 years ago
CIIE

Bikin baje kolin kayayyakin da ake shigowa da su kasar Sin na duniya (CIIE) ya nuna kudurin kasar Sin na hada kan duniya domin cin gajiyar juna ta fuskar tattalin arziki har ma da zamantakewa.

A karon farko da na samu labarin bikin, na yi tunanin akwai yiwuwar za a bar ’yan kasuwarmu na Afirka da dama a baya wurin shiga a dama da su, saboda rashin karfin jari irin na takwarorinsu na sauran duniya.

  • Xi Zai Gana Da Biden Tare Da Halartar Taron Shugabannin Tattalin Arzikin APEC
  • Sin Na Taka Rawar Gani Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya A Gabas Ta Tsakiya

Amma bisa bayanan da na ji daga cibiyar baje kolin, a ziyararmu ta aiki a 2018 a Shanghai, shugabannin shiryawa sun ce, baje kolin na CIIE ya tsara taimakawa kasashe masu rauni wajen ba su matsugunai domin baje kolinsu ba tare da biyan kudi ba har ma da wani tallafi da zai taimaka wa kayayyakinsu su samu damar shiga kasuwar kasar Sin.

Wannan tsari ya haifar da da mai ido, domin ko a bana, daga kasar Zimbabwe kawai, fiye da kamfanoni da kungiyoyi 15 da suka kware a fannin fasahar zane, da sarrafa kayayyakin fata, da harkokin sadarwa, da kuma sayar da ma’adanai, suke halartar bikin baje kolin.

Haka nan daga Nijeriya da Afirka ta Kudu da sauran kasashe duk suna can ana damawa da su a bikin baje kolin na bana karo na 6 a birnin Shanghai.

LABARAI MASU NASABA

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

Baje kolin na CIIE, karin dama ce ga Nijeriya ta samun cinikin kayan da take fitarwa zuwa Sin kamar su kwarar manja, ridi, ‘ya’yan itace, hatsi har ma da waken soya wanda cinikayyarsu sun kai Dalar Amurka miliyan 140.88 a shekarar 2021, bisa bayanan cibiyar cinikayya ta COMTRADE ta Majalisar Dinkin Duniya.

Shugaban Tsangayar Aikin Gona da Raya Karkara ta ARMTI da ke Nijeriya, Dr. Olufemi Oladunni, ya bayyana cewa, “akwai damammaki da yawa da manoman Nijeriya za su ci gajiya a kasuwanni na kasashen duniya bisa cudanya da ‘yan kasuwa na waje, manoman za su samu dabarun inganta noma, da yadda za su rika sarrafa amfanin gona bayan girbi da kuma fitarwa waje.”
Har ila yau, manajan daraktar kamfanin sarrafa kayan fata na Samuneti dake Zimbabwe, Tsitsi Chirova, ta ce baje kolin CIIE fage ne da suke samun damar fadada hadin gwiwa da kara fahimtar ire-iren kayayyakin da za su rika sarrafawa. “Daga shigar da muka yi a baya, mun sami damar habaka tallace-tallacenmu, da kuma samun shawarwari daga abokan cinikinmu don habaka abubuwan da muke samarwa. Don haka idan muka halarci bikin baje kolin na kasar Sin, na yi imani hakan zai tallata kamfaninmu da gaske, kuma bayan mun dawo gida, mun yi imanin za mu samu karin kwastomomi,” in ji ta.

Shi ma wani mai sassaka dake birnin Harare, Richard Mudinzva, da ya sha alwashin halartar bikin karo na 6, ya ce, akwai abokan ciniki da yawa a kasuwar kasar Sin dake sha’awar kayayyakin Afirka. Alkaluman da ofishin jakadancin kasar Sin dake Zimbabwe ya fitar sun nuna cewa, cinikayyar bangarorin biyu ta karu da kashi 39.4 bisa dari, zuwa dala biliyan 2.43 daga Janairu zuwa Satumbar 2023, wanda ya zarce adadin cinikin da aka samu a shekarar 2022.

Kasar Guinea-Bissau, mafi noman kashu a duniya, ta ci gajiyar bikin baje kolin a bara, yayin da aka ware mata matsugunin kamfanoninta suka baje kolinsu na kashu. Kamar yadda jakadan kasar a Sin, Antonio Serifo Embalo ya bayyana, sakamakon halartar bikin baje kolin na bara, ’yan kasuwa da dama sun nuna muradinsu a kan bangaren kashu na kasar. Wasu ma tuni har sun tsara yadda za su zuba jari a kasar.
A nashi bangaren, mataimakin shugaban Afirka ta Kudu, Paul Mashatile, ya yaba wa kasar Sin bisa yadda take kara bude kofofinta na kasuwanci musamman ga kasashen Afirka. Yana mai cewar, bikin baje kolin ya kara fadada dama ga kamfanoni na duniya wajen bunkasa hulda da abokan ciniki.

Sama da kamfanoni 1,500 daga kasashen dake cikin shawarar “ziri daya da hanya daya” ke baje kolin hajojinsu a bikin karo na shida.

Ana sa rai, cinikayyar shigo da kaya na kasar Sin su zarce dala tiriliyan 17 nan da shekara 5 masu zuwa, don haka nake cewa, kasashen Afirka kar ku yarda a bar ku a baya wajen cin gajiyar hakan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan
Daga Birnin Sin

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

October 25, 2025
Next Post
Taj

Bankin TAJ Ya Sake Lashe Kyautar Gwarzon Bankin Musulunci Na Bana

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ɗan Majalisa Na Shekarar 2025: Benjamin Okezie Kalu

October 26, 2025
An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

October 25, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

October 25, 2025
Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

October 25, 2025
An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

October 25, 2025

Daɓid Adeyemi

October 25, 2025
Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.